< Irmiya 14 >
1 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya game da fări cewa,
Detta är det ord, som Herren till Jeremia sade, om den dyra tiden:
2 “Yahuda tana makoki biranenta suna fama; suna kuka saboda ƙasar, kuka kuma tana tasowa daga Urushalima.
Juda ligger jämmerliga, hans portar stå i en ömkelig måtto; det står klageliga till i landena, och i Jerusalem är ett stort rop.
3 Manyan mutane suna aika bayinsu su ɗebo ruwa a maɓulɓulai amma babu ruwa. Suka dawo da tulunansu haka nan; da kunya da kuma ƙasƙanci, da kawunansu a rufe.
De store sända de små efter vatten; men då de komma till brunnen, så finna de intet vatten, och bära sina käril tom hem igen; de gå sorgse och bedröfvade, och omsvepa sin hufvud;
4 Ƙasa ta tsattsage saboda babu ruwan sama a ƙasar; manoma sun sha kunya suka kuma rufe kawunansu.
Derföre, att jorden refnar, efter intet regnar på jordena; åkermännerna, gå sorgse, och omsvepa sin hufvud.
5 Har barewa a kurmi ma ta gudu ta bar’ya’yan da ta haihu sababbi saboda babu ciyawa.
Ty ock hinderna, som på markena kalfva, öfvergifva sina kalfvar, efter intet gräs växer.
6 Jakan jeji suna tsaye a kan tuddai suna haki kamar diloli; idanunsu sun kāsa gani saboda rashin makiyaya.”
Vildåsnarna stå på bergen, och lukta efter vädret, lika som drakar, och försmäkta, efter ingen ört växer.
7 Ko da yake zunubanmu suna ba da shaida a kanmu, Ya Ubangiji, ka yi wani abu saboda sunanka. Gama jan bayanmu ya yi yawa; mun yi maka zunubi.
Ack! Herre, våra missgerningar hafva det ju förtjent; men hjelp dock för ditt Namns skull; ty vår ohörighet är stor, der vi emot dig med syndat hafve.
8 Ya kai, Sa Zuciyar Isra’ila, Mai Cetonsa a lokutan wahala, me ya sa kake yi kamar baƙo a ƙasar, kamar matafiyi wanda yake shirya wuri don yă kwana gari ya waye ya wuce?
Du äst Israels tröst, och hans nödhjelpare; hvi skickar du dig, lika som du vore främmande i landena, och såsom en gäst, den icke mer än ena natt derinne ligger?
9 Me ya sa kake yi kamar mutumin da aka far masa kwasam ba zato, kamar jarumi marar ƙarfin ceto? Kana a cikinmu, ya Ubangiji, da sunanka ake kiranmu; kada ka yashe mu!
Hvi hafver du dig såsom en hjelte, som förtviflad är; och som en kämpe, den intet hjelpa kan? Du äst ju dock ibland oss, Herre, och vi nämnes efter ditt Namn; öfvergif oss icke.
10 Ga abin da Ubangiji ya ce game da wannan mutane, “Suna son yawace-yawace ƙwarai; ba sa hana ƙafafunsu yawo. Saboda haka Ubangiji bai yarda da su ba; yanzu zai tuna da muguntarsu zai kuma hukunta su saboda zunubansu.”
Så säger Herren om detta folket: De löpa gerna hit och dit, och blifva icke gerna hemma; derföre hafver Herren ingen vilja till dem; utan han tänker nu uppå deras missgerningar, och vill hemsöka deras synder.
11 Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, “Kada ka yi addu’a domin zaman lafiyar mutanen nan.
Och Herren sade till mig: Du skall intet bedja för detta folk om nåde.
12 Ko da yake suna azumi, ba zan saurari kukansu ba, ko da yake suna miƙa hadayun ƙonawa da hadayun gari, ba zan yarda da su ba. A maimako zan hallaka su da takobi, yunwa da annoba.”
Ty om de än fastade, så vill jag dock intet höra deras bön; och om de än hade bränneoffer och spisoffer fram, så behaga de mig dock intet; utan jag vill göra en ända uppå dem med svärd, hunger och pestilentie.
13 Amma na ce, “A, Ubangiji Mai Iko Duka, annabawa sun riƙa ce musu, ‘Ba za ku ga takobi ko ku yi fama da yunwa ba. A maimako, zan ba ku madawwamiyar salama.’”
Då sade jag: Ack Herre Herre! Si, Propheterna säga dem: I skolen intet svärd se, och ingen dyr tid få när eder; men jag skall gifva eder en god frid i detta rummet.
14 Sai Ubangiji ya ce mini, “Annabawa suna ta annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba, ban kuma naɗa su ba, ban yi musu magana ba. Suna muku annabci wahayin ƙarya, suna muku duba marar amfani, suna bautar gumaka suna kuma bayyana tunanin kansu ne.
Och Herren sade till mig: Propheterna, spå lögn i mitt Namn; jag hafver intet sändt dem, och intet befallt dem, och intet talat med dem; de predika eder falska syner, spådom, afguderi, och sins hjertans bedrägeri.
15 Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce game da annabawan da suke annabci da sunana. Ban aike su ba, duk da haka suna cewa, ‘Babu takobi ko yunwar da zai taɓa wannan ƙasa.’ Waɗannan annabawa takobi da yunwa za su hallaka su.
Derföre säger Herren om de Propheter, som i mitt Namn prophetera, ändock jag dem intet sändt hafver, och de likväl predika, att intet svärd eller dyr tid skall komma i detta land: Sådana Propheter skola dö genom svärd och hunger.
16 Mutanen da suke musu annabcin kuwa za a kore su zuwa titunan Urushalima saboda yunwa da kuma takobi. Babu wanda zai binne su, ko ya binne matansu, ko’ya’yansu maza da mata. Zan aukar musu da masifar da ya dace da su.
Och folket, hvilko de prophetera, skola af svärd och hunger ligga här och der på gatomen i Jerusalem, att ingen skall begrafva dem; sammalunda ock deras hustrur, söner och döttrar; och jag skall gjuta deras ondsko uppå dem.
17 “Ka yi musu wannan magana, “‘Bari idanuna su yi ta zub da hawaye dare da rana kada su daina; saboda’yata budurwa, mutanena, sun sha wahalar babban rauni, an yi musu bugu mai ragargazawa.
Och du skall säga till dem detta ordet: Min ögon flyta med tårar dag och natt, och vända intet åter; ty jungfrun, mins folks dotter, är grufveliga plågad, och jämmerliga slagen.
18 In na shiga cikin ƙasar, na ga waɗanda takobi ya kashe; in na shiga cikin birni, na ga waɗanda suke fama da yunwa. Da Annabi da firist duk sun tafi ƙasar da ba su sani ba.’”
Går jag ut på markena, si, så ligga der de slagne med svärd; kommer jag in uti staden, så ligga der de försmäktade af hunger; ty ock Propheterna och Presterna måste bortdraga uti ett land, det de intet känna.
19 Ka ƙi Yahuda ɗungum ke nan? Kana ƙyamar Sihiyona ne? Me ya sa ka buge mu don kada mu warke? Mun sa zuciya ga salama babu abin alherin da ya zo, mun sa rai ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
Hafver du då förkastat Juda? Eller hafver din själ en vämjelse till Zion? Hvi hafver du så slagit oss, att oss ingen hela kan? Vi hoppades, att det skulle frid varda, men här kommer intet godt; vi hoppades, att vi skulle helade varda, och si, här är nu mera vedermöda.
20 Ya Ubangiji, mun gane da muguntarmu da kuma laifin kakanninmu; tabbatacce mun yi maka zunubi.
Herre, vi kännom vårt ogudaktiga väsende, och våra fäders missgerningar; ty vi hafve syndat emot dig.
21 Saboda sunanka kada ka ƙi mu; kada ka ƙasƙantar da kursiyoyinka mai ɗaukaka. Ka tuna da alkawarinka da mu kada ka tā da shi.
Men, för ditt Namns skull, låt oss icke skämde varda; låt dine härlighets säte icke begabbadt varda; kom dock ihåg, och låt icke ditt förbund med oss återvända.
22 Akwai wani daga cikin gumaka marasa amfani na al’ummai da ya kawo ruwan sama? Sararin sama kansu sukan yi yayyafi? A’a, kai ne, ya Ubangiji Allahnmu. Saboda haka sa zuciyarmu tana a kanka, gama kai ne kake yi wannan duka.
Det är dock ingen ibland Hedningarnas afgudar, som regn gifva kan; himmelen kan ock icke regna. Du äst ju Herren vår Gud, uppå hvilken vi hoppas; ty du kan alltsammans detta göra.