< Irmiya 10 >
1 Ku ji abin da Ubangiji yana ce muku, ya gidan Isra’ila.
Listen to the message the Lord is sending to you, people of Israel.
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ku koyi hanyoyin al’ummai ko ku razana game da alamun sararin sama, ko da yake al’ummai sun razana saboda su.
This is what the Lord says: Don't adopt the practices of other nations. Don't be terrified as they are by signs in the heavens that they interpret as predicting disaster.
3 Gama al’adun mutane banza ne; sukan yanke itace daga kurmi, sai mai sassaƙa yă sassaƙa shi da gizago.
The religious beliefs of the peoples are pointless. They chop down a tree in the forest and a craftsman carves the wood with a tool to make an idol.
4 Sukan yi masa ado da azurfa da kuma zinariya; sukan ɗauki guduma su kafa shi da ƙusoshi, don kada yă fāɗi.
They decorate it with silver and gold, and nail it down with a hammer so it won't fall over.
5 Kamar dodon gona cikin gonar kabewa, haka gumakansu ba sa iya magana; dole a yi ta ɗaukansu domin ba za su iya tafiya ba. Kada ku ji tsoronsu; ba za su iya yi wa wani lahani ba ba sa iya yin wani abin kirki.”
Just like a scarecrow in a field of cucumbers, their idols can't speak. They have to be carried around because they can't walk. You don't have to be afraid of them because they can't hurt you—and they can't do you any good either.
6 Babu wani kamar ka, ya Ubangiji; kai mai girma ne, kuma sunanka yana da girma da kuma iko.
There's no one like you, Lord! You are so great! You are incredibly powerful!
7 Wane ne ba zai girmama ka ba, Ya Sarkin al’ummai? Tsoronka wajibi ne. A cikin dukan masu hikima na al’ummai kuma cikin dukan mulkokinsu, babu kamar ka.
Everyone should respect you, King of the nations. This is how you should be treated. There's no one like you among all the wise men of every nation and kingdom.
8 Dukansu marasa azanci ne wawaye; gumakan itacen banza ne suke koya musu.
Yet these “wise men” are completely foolish and stupid, because they think they can be taught by useless idols made of wood!
9 An kawo ƙeraren azurfa daga Tarshish zinariya kuma daga Ufaz. Abin da gwani da maƙerin zinariya suka yi sa’an nan aka yi masa ado da mulufi da shunayya dukan aikin gwanaye.
Sheets of hammered silver are shipped in from Tarshish, and gold from Uphaz, to be used by craftsmen and metalworkers. These idols are dressed in clothes of blue and purple made by experts.
10 Amma Ubangiji shi ne Allah na gaskiya; shi ne Allah mai rai, madawwamin sarki. Sa’ad da ya yi fushi, ƙasa takan girgiza; al’ummai ba sa iya jure da hasalarsa.
But the Lord is the only true God. He is the living God and eternal King. The earth shakes when he is angry; the nations can't withstand his fury.
11 “Ka faɗa musu wannan, ‘Waɗannan alloli, waɗanda ba su yi sammai da ƙasa ba, za su hallaka daga duniya da kuma daga ƙarƙashin sammai.’”
This is what you are to tell the nations: “These gods, who didn't make either the heavens or the earth, will be wiped out from this earth and from under these heavens.”
12 Amma Allah ya yi duniya ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa ya shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
It was God who made the earth by his power. He created the world by his wisdom and by his understanding he put the heavens in place.
13 Sa’ad da ya yi tsawa, ruwaye a cikin sammai sukan yi ƙugi; yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya. Yakan aiki walƙiya da ruwan sama ya fitar da iska daga gidajen ajiyarsa.
The waters of the heavens rain down with a roar at his command. He makes the clouds to rise all over the earth. He makes lightning to accompany rain, and sends the wind from his storehouses.
14 Kowa marar azanci ne, marar ilimi; kowane maƙerin zinariya zai sha kunya saboda gumakansa. Siffofinsa ƙarya ne; ba su da numfashi a cikinsu.
Everyone is stupid; they don't know anything. Every metalworker is embarrassed by the idols they make. For their images made of molten metal are fraudulent—they're not alive!
15 Su ba kome ba ne, aikin ruɗami ne; Sa’ad da hukuncinsu ya yi za su lalace.
They are useless, an object to be laughed at. They will be destroyed at the time of their punishment.
16 Shi da yake Rabon Yaƙub ba kamar waɗannan yake ba, gama shi ne Mahaliccin abubuwa duka, har da Isra’ila, kabilar gādonsa Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
The God of Jacob is not like these idols, for he is the Creator of everything, and Israel is the tribe that belongs to him. The Lord Almighty is his name.
17 Ku tattara kayayyakinku don ku bar ƙasar, ku da kuke zaune a wurin da aka kewaye da yaƙi.
You people living in Jerusalem under siege, get all your things together ready to leave,
18 Gama haka Ubangiji ya faɗa, “A wannan lokaci zan jefar da waɗanda suke zaune a ƙasar; zan kawo damuwa a kansu domin a kama su.”
because this is what the Lord says: Look! Right now I'm about to throw out the people living in this country, bringing them trouble they will really feel.
19 Tawa ta ƙare, saboda raunin da aka yi mini! Raunina ba mai warkewa ba ne! Duk da haka na ce wa kaina, “Wannan ciwona ne, dole kuma in jure da shi.”
The people of Jerusalem responded, “We're suffering terribly because we've been badly hurt—our injuries are really serious. We thought it wouldn't be that bad and that we could bear it.
20 An lalatar da tentina; dukan igiyoyinsa sun tsintsinke.’Ya’yana maza sun bar ni ba sa nan; ba wanda aka bari da zai kafa tentina ko ya kafa mini mafaka.
Our tents have been destroyed; all our ropes have been broken. Our children have been taken from us and are no more. We don't have anyone left to put up our tents or hang our curtains.”
21 Makiyaya marasa azanci ne kuma ba sa neman nufin Ubangiji; saboda haka ba sa nasara dukan garkensu kuwa ya watse.
The “shepherds” have become stupid—they don't ask the Lord for advice. That's why they have failed, and all their flock has been scattered.
22 Ku saurara! Rahoto yana zuwa babban hargitsi daga ƙasar arewa! Zai mai da garuruwan Yahuda kufai, mazaunin diloli.
Listen to the news that an noisy army is invading from a country to the north. The towns of Judah will be knocked down, they will be places where only jackals live.
23 Na sani, ya Ubangiji, cewa ran mutum ba nasa ba ne; ba mutum ne yake kiyaye takawarsa ba.
I realize, Lord, that people don't control their own lives—no one really knows how to choose their way.
24 Ka yi mini gyara, Ubangiji, amma fa da adalci kaɗai ba cikin fushinka ba, don kada ka wofinta ni.
Please discipline me fairly, Lord—not while you're angry, otherwise you'll kill me!
25 Ka zuba hasalarka a kan al’umman da ba su san ka ba, a kan mutanen da ba sa kira bisa sunanka. Gama sun cinye Yaƙub; sun cinye shi gaba ɗaya suka kuma lalace wurin zamansa.
Pour out your fury on the nations that don't recognize you as God, and on their families that don't worship you. For they have completely destroyed the Israelites, wiping us out. They have devastated our country.