< Ishaya 64 >

1 Da ma za ka tsage sammai ka sauko, ai, da duwatsu za su yi rawar jiki a gabanka!
Did You not tear the heavens? You came down, Mountains flowed from Your presence,
2 Kamar sa’ad da wuta takan ci rassa ta sa ruwa ya tafasa, ka sauko ka sanar da sunanka ga abokan gābanka ka kuma sa al’ummai su yi rawan jiki a gabanka!
(As fire kindles stubble—Fire causes water to boil), To make Your Name known to Your adversaries, Nations tremble from Your presence.
3 Gama sa’ad da ka aikata abubuwan bantsoron da ba mu sa tsammani ba, ka sauko, duwatsu kuma suka yi rawar jiki a gabanka.
In Your doing fearful things [that] we do not expect, You came down, Mountains flowed from Your presence.
4 Tun fil azal babu wanda ya taɓa ji, babu kunnen da ya gane, babu idon da ya ga wani Allah in ban da kai, wanda ya aikata waɗannan al’amura a madadin waɗanda suke sa zuciya a gare shi.
Even from antiquity [men] have not heard, They have not given ear, Eye has not seen a God except You, He works for those waiting for Him.
5 Kakan taimaki waɗanda suke murnan yin abin da yake daidai, waɗanda sukan tuna da hanyoyinka. Amma sa’ad da muka ci gaba da yin zunubi, kakan yi fushi. Ta yaya za mu sami ceto ke nan?
You have met with the rejoicer And the doer of righteousness, In Your ways they remember You, Behold, You have been angry when we sin, By them [is] continuance, and we are saved.
6 Dukanmu mun zama kamar wanda yake marar tsabta, kuma dukan ayyukanmu masu adalci sun zama kamar ƙazaman tsummoki; duk mun zama kamar busasshen ganye, kamar iska haka zunubanmu sukan share mu.
And we are as unclean—all of us, And all our righteous acts [are] as garments of menstruation; And we fade as a leaf—all of us. And our iniquities take us away as wind.
7 Babu wanda yake kira bisa sunanka ko ya yi ƙoƙarin riƙe ka; gama ka ɓoye fuskarka daga gare mu ka kuma sa muka lalace saboda zunubanmu.
And there is none calling on Your Name, Stirring himself up to lay hold on You, For You have hid Your face from us, And You melt us away by our iniquities.
8 Duk da haka, Ubangiji, kai ne Ubanmu. Mu yumɓu ne, kai kuma mai ginin tukwane; dukanmu aikin hannunka ne.
And now, O YHWH, You [are] our Father, We [are] the clay, and You [are] our Framer, And the work of Your hand—all of us.
9 Kada ka yi fushi fiye da kima, ya Ubangiji; kada ka tuna da zunubanmu har abada. Da ma ka dube mu, muna roƙonka, gama dukanmu mutanenka ne.
Do not be angry, O YHWH, very severely, Nor remember iniquity forever, Behold, look attentively, we implore You, We [are] all Your people.
10 Biranenka masu tsarki sun zama hamada; har Sihiyona ma ta zama hamada; Urushalima ta zama kango.
Your holy cities have been a wilderness, Zion has been a wilderness, Jerusalem a desolation.
11 Haikalinmu mai tsarki da kuma mai daraja, inda kakanninmu suka yabe ka, an ƙone da wuta, kuma dukan abubuwan da muke ƙauna sun lalace.
Our holy and our beautiful house, Where our fathers praised You, Has become burned with fire, And all our desirable things have become a ruin.
12 Bayan dukan wannan, ya Ubangiji, ba za ka yi wani abu ba? Za ka yi shiru ka hore mu fiye da kima?
Do You refrain Yourself for these, YHWH? You are silent, and afflict us very severely!

< Ishaya 64 >