< Ishaya 63 >

1 Wane ne wannan mai zuwa daga Edom, daga Bozra, saye da jajjayen rigunarsa? Wane ne wannan, sanye cikin daraja, tafe cikin girmar ƙarfinsa? “Ni ne, mai magana cikin adalci, mai ikon ceto.”
Who [is] this coming from Edom? With dyed garments from Bozrah? This that is honorable in His clothing, Traveling in the abundance of His power? “I, speaking in righteousness, mighty to save.”
2 Me ya sa rigunanka suka yi ja, sai ka ce na wanda yake tattaka’ya’yan inabi?
Why [is] Your clothing red? And Your garments as treading in a winepress?
3 “Na tattake’ya’yan inabi ni kaɗai; cikin al’ummai kuma babu wani tare da ni. Na tattake su cikin fushina Na matse su cikin hasalata; jininsu ya fantsamar wa rigunana, na kuma ɓata dukan tufafina.
“I have trodden a wine vat by Myself, And of the peoples there is no one with Me, And I tread them in My anger, And I trample them in My fury, Their strength is sprinkled on My garments, And I have defiled all My clothing.
4 Gama ranar ɗaukan fansa tana a cikin zuciyata, kuma shekarar fansata ta zo.
For the day of vengeance [is] in My heart, And the year of My redeemed has come.
5 Na duba, amma babu wanda zai taimaka, na yi mamaki cewa ba wanda ya goyi baya; saboda haka hannuna ya yi mini ceto, fushina kuma ya rayar da ni.
And I look attentively, and there is none helping, And I am astonished that there is none supporting, And My own arm gives salvation to Me. And My wrath—it has supported Me.
6 Na tattake al’ummai cikin fushina; cikin hasalata kuma na sa sun bugu na kuma zub da jininsu a ƙasa.”
And I tread down peoples in My anger, And I make them drunk in My fury, And I bring down their strength to earth.”
7 Zan ba da labarin alherin Ubangiji, ayyukan da suka sa a yabe shi, bisa ga dukan abubuwan da Ubangiji ya yi mana, I, ayyuka masu kyan da ya yi domin gidan Isra’ila, bisa ga jinƙansa da yawan alheransa.
I make mention of the kind acts of YHWH, The praises of YHWH, According to all that YHWH has done for us, And the abundance of the goodness to the house of Israel, That He has done for them, According to His mercies, And according to the abundance of His kind acts.
8 Ya ce, “Babu shakka su mutanena ne,’ya’ya maza waɗanda ba za su ruɗe ni ba”; ta haka ya zama Mai Cetonsu.
And He says, “Surely they [are] My people, Sons—they do not lie,” and He is to them for a Savior.
9 Cikin dukan damuwarsu shi ma ya damu, mala’ikan da yake gabansa ya cece su. Cikin ƙauna da jinƙai ya fanshe su; ya kuma ɗaga su ya riƙe su dukan kwanakin dā
In all their distress [He is] no adversary, And the Messenger of His Presence saved them, In His love and in His pity He redeemed them, And He lifts them up, And carries them all the days of old.
10 Duk da haka suka yi tawaye suka ɓata wa Ruhu Mai Tsarki rai. Saboda haka ya juya ya kuma zama abokin gābansu shi kansa kuma ya yaƙe su.
And they have been rebellious and have grieved His Holy Spirit, And He turns to them for an enemy, He Himself has fought against them.
11 Sa’an nan mutanensa suka tuna kwanakin dā, kwanakin Musa da mutanensa, ina yake shi wanda ya fitar da su ta teku, da makiyayan garkensa? Ina shi yake wanda ya sa Ruhunsa Mai Tsarki a cikinsu,
And He remembers the days of old, Moses—his people. Where [is] He who is bringing them up from the sea, The shepherd of His flock? Where [is] He who is putting in its midst His Holy Spirit?
12 wanda ya aika hannu ɗaukakarsa mai iko ya kasance a hannun dama na Musa, wanda ya raba ruwaye a gabansu, don yă sami wa kansa madawwamin suna,
Leading by the right hand of Moses, the arm of His glory, Cleaving waters from before them, To make to Himself a continuous Name.
13 wanda ya bishe su cikin zurfafa? Kamar doki a fili, ba su yi tuntuɓe ba;
Leading them through the depths, They do not stumble as a horse in a plain.
14 kamar shanun da suke gangarawa zuwa kwari, haka Ruhun Ubangiji ya ba su hutu. Ga yadda ka bishe mutanenka don ka ba wa kanka suna mai ɗaukaka.
As a beast goes down into a valley, The Spirit of YHWH causes him to rest, So You have led Your people, To make to Yourself a glorious Name.
15 Ka duba daga sama ka gani daga kursiyinka da yake bisa, mai tsarki da kuma mai ɗaukaka. Ina kishinka da kuma ikonka? Ka janye juyayi da kuma tausayin da kake yi mana daga gare mu.
Look attentively from the heavens, And see from Your holy and beautiful habitation, Where [is] Your zeal and Your might? The multitude of Your bowels and Your mercies—Are they restrained?
16 Amma kai Ubanmu ne, ko Ibrahim bai san mu ba Isra’ila kuma bai yarda da mu ba; kai, ya Ubangiji, kai ne Ubanmu, Mai Fansarmu tun fil azal ne sunanka.
For You [are] our Father, For Abraham has not known us, And Israel does not acknowledge us, You, O YHWH, [are] our Father, Our Redeemer from the Age, [is] Your Name.
17 Don me, ya Ubangiji, ka sa muna barin hanyoyinka muka kuma taurare zukatanmu don kada mu girmama ka? Ka komo domin darajar bayinka, kabilan da suke abin gādonka.
Why cause us to wander, O YHWH, from Your ways? You harden our heart from Your fear, Turn back for Your servants’ sake, The tribes of Your inheritance.
18 Gama a ɗan lokaci mutanenka suka mallaki wurinka mai tsarki, amma yanzu abokan gābanmu sun tattake wurinka mai tsarki.
For a little while Your holy people possessed, Our adversaries have trodden down Your sanctuary.
19 Mu naka tun fil azal; ba ka taɓa yin mulki a kansu ba, ba a taɓa kira su da sunanka ba.
We have been from of old, You have not ruled over them, Your Name is not called on them!

< Ishaya 63 >