< Ishaya 61 >

1 Ruhun Ubangiji Mai Iko Duka yana a kaina, domin Ubangiji ya shafe ni domin in yi wa’azi labari mai daɗi ga matalauta. Ya aiko ni in warkar da waɗanda suka karai a zuci, don in yi shelar’yanci don ɗaurarru in kuma kunce’yan kurkuku daga duhu
“[The] Spirit of Lord YHWH [is] on Me, Because YHWH anointed Me To proclaim tidings to the humble, He sent Me to bind the broken of heart, To proclaim liberty to the captives, And an opening of bands to [those] bound.
2 don in yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji da kuma ranar ɗaukan fansar Allahnmu, don in ta’azantar da dukan waɗanda suke makoki,
To proclaim the year of the favor of YHWH, And the day of vengeance of our God, To comfort all mourners.
3 in tanada wa waɗanda suke baƙin ciki a Sihiyona, in maido musu rawani mai kyau a maimako na toka, man murna a maimako na makoki, da kuma rigar yabo a maimako na ruhun fid da zuciya. Za a ce da su itatuwan oak na adalci, shukin Ubangiji don bayyana darajarsa.
To appoint to mourners in Zion, To give to them beauty instead of ashes, The oil of joy instead of mourning, A covering of praise for a faded spirit, And He is calling to them, Trees of righteousness, The planting of YHWH—to be beautified.”
4 Za su sāke gina kufai na dā su raya wurare da aka lalace tun da daɗewa; za su sabunta biranen da aka rurrushe da aka lalace tun zamanai masu yawa da suka wuce.
And they have built the ancient ruins, They raise up the desolations of the ancients, And they have renewed ruined cities, The desolations of generation and generation.
5 Baƙi za su yi kiwon garkunanki; baƙi za su yi miki noman gonaki da gonakin inabinki.
And strangers have stood and fed your flock, And the sons of a foreigner [Are] your farmers and your vinedressers.
6 Za a kuma kira ku firistocin Ubangiji, za a kira ku masu hidimar Allahnmu. Za ku ci wadatar waɗansu al’ummai, kuma a cikin dukiyarsu za ku yi taƙama.
And you are called priests of YHWH, It is said of you [that you are] ministers of our God, You consume the strength of nations, And you boast yourselves in their glory.
7 A maimakon kunyarsu mutanena za su sami rabi riɓi biyu, a maimakon wulaƙanci za su yi farin ciki cikin gādonsu; ta haka za su gāji rabo riɓi biyu a ƙasarsu, da kuma madawwamin farin ciki zai zama nasu.
Instead of your shame—double [honor], And [instead of] confusion, They rejoice in their portion, Therefore they take possession in their land a second time, Continuous joy [is] for them.
8 “Gama ni, Ubangiji, ina ƙaunar adalci; na ƙi fashi da aikata laifi. Cikin adalcina zan sāka musu in kuma yi madawwamin alkawari da su.
“For I [am] YHWH, loving judgment, Hating plunder for a burnt-offering, And I have given their wage in truth, And I make a perpetual covenant for them.
9 Za a san da zuriyarsu a cikin al’ummai’ya’yansu kuma a cikin mutane. Dukan waɗanda suka gan su za su san cewa su mutane ne da Ubangiji ya sa wa albarka.”
And their seed has been known among the nations, And their offspring in the midst of the peoples, All their beholders acknowledge them, For they [are] a seed YHWH has blessed.”
10 Ina jin daɗi ƙwarai a cikin Ubangiji; raina yana farin ciki a cikin Allahna. Gama ya suturce ni da rigunan ceto ya yi mini ado da rigar adalci, yadda ango yakan yi wa kansa ado kamar firist kamar kuma yadda amarya takan sha ado da duwatsunta masu daraja.
I greatly rejoice in YHWH, My soul rejoices in my God, For He clothed me with garments of salvation, [And] covered me with a robe of righteousness, As a bridegroom prepares ornaments, And as a bride puts on her jewels.
11 Gama kamar yadda ƙasa takan sa tsire-tsire su tohu lambu kuma ya sa iri ya yi girma, haka Ubangiji Mai Iko Duka zai sa adalci da yabo su tsiro a gaban dukan al’ummai.
For as the earth brings forth her shoots, And as a garden causes its sown things to shoot up, So Lord YHWH causes righteousness and praise To shoot up before all the nations!

< Ishaya 61 >