< Ishaya 61 >
1 Ruhun Ubangiji Mai Iko Duka yana a kaina, domin Ubangiji ya shafe ni domin in yi wa’azi labari mai daɗi ga matalauta. Ya aiko ni in warkar da waɗanda suka karai a zuci, don in yi shelar’yanci don ɗaurarru in kuma kunce’yan kurkuku daga duhu
The Spirit of the Lord Eternal is upon me; because the Lord hath anointed me to announce good tidings unto the meek: he hath sent me to bind up the broken-hearted, to proclaim to captives Liberty, and to prisoners Release;
2 don in yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji da kuma ranar ɗaukan fansar Allahnmu, don in ta’azantar da dukan waɗanda suke makoki,
To proclaim a year of favor of the Lord, and the day of vengeance of our God, to comfort all mourners;
3 in tanada wa waɗanda suke baƙin ciki a Sihiyona, in maido musu rawani mai kyau a maimako na toka, man murna a maimako na makoki, da kuma rigar yabo a maimako na ruhun fid da zuciya. Za a ce da su itatuwan oak na adalci, shukin Ubangiji don bayyana darajarsa.
To grant unto the mourners of Zion, —to give unto them ornament in the place of ashes, oil of gladness in the place of mourning, garments of praise in the place of a grieved spirit; that they may be called, Oaks of righteousness, the planting of the Lord, that he may be glorified.
4 Za su sāke gina kufai na dā su raya wurare da aka lalace tun da daɗewa; za su sabunta biranen da aka rurrushe da aka lalace tun zamanai masu yawa da suka wuce.
And they shall build up the ancient ruins, desolate places of former times shall they raise up, and they shall renew ruined cities, the desolate places of many generations.
5 Baƙi za su yi kiwon garkunanki; baƙi za su yi miki noman gonaki da gonakin inabinki.
And strangers shall stand and feed your flocks, and the sons of the alien shall be your ploughmen and your vintners.
6 Za a kuma kira ku firistocin Ubangiji, za a kira ku masu hidimar Allahnmu. Za ku ci wadatar waɗansu al’ummai, kuma a cikin dukiyarsu za ku yi taƙama.
But ye, ye shall be called, Priests of the Lord; Ministers of our God, shall be said unto you: the wealth of nations shall ye consume, and in their glory shall ye be placed as possessors.
7 A maimakon kunyarsu mutanena za su sami rabi riɓi biyu, a maimakon wulaƙanci za su yi farin ciki cikin gādonsu; ta haka za su gāji rabo riɓi biyu a ƙasarsu, da kuma madawwamin farin ciki zai zama nasu.
In the place of your twofold shame, —and the confusion of which they loudly complained as their portion: therefore in their land shall they possess a twofold [portion]; everlasting joy shall be granted unto them.
8 “Gama ni, Ubangiji, ina ƙaunar adalci; na ƙi fashi da aikata laifi. Cikin adalcina zan sāka musu in kuma yi madawwamin alkawari da su.
For I the Lord love justice, I hate robbery with burnt-offering: therefore will I give them the recompense of their work in truth, and an everlasting covenant will I make with them.
9 Za a san da zuriyarsu a cikin al’ummai’ya’yansu kuma a cikin mutane. Dukan waɗanda suka gan su za su san cewa su mutane ne da Ubangiji ya sa wa albarka.”
And among the nations shall their seed be known, and their offspring in the midst of the people: all that see them shall acknowledge them, that they are the seed whom the Lord hath blessed.
10 Ina jin daɗi ƙwarai a cikin Ubangiji; raina yana farin ciki a cikin Allahna. Gama ya suturce ni da rigunan ceto ya yi mini ado da rigar adalci, yadda ango yakan yi wa kansa ado kamar firist kamar kuma yadda amarya takan sha ado da duwatsunta masu daraja.
I will be greatly glad in the Lord, my soul shall be joyful in my God; for he hath clothed me with the garments of salvation, with the mantle of righteousness hath he enveloped me, as a bridegroom decketh himself with elegant attire, and as a bride adorneth herself with her bridal array.
11 Gama kamar yadda ƙasa takan sa tsire-tsire su tohu lambu kuma ya sa iri ya yi girma, haka Ubangiji Mai Iko Duka zai sa adalci da yabo su tsiro a gaban dukan al’ummai.
For, as the earth bringeth forth her growth, and as a garden causeth what is sown therein to spring forth: thus will the Lord Eternal cause righteousness and praise to spring forth in the presence of all the nations.