< Ishaya 59 >

1 Tabbatacce hannun Ubangiji bai kāsa yin ceto ba, kunnensa kuma bai kurmance da zai kāsa ji ba.
Ne, nije ruka Jahvina prekratka da spasi, niti mu je uho otvrdlo da ne bi čuo,
2 Amma laifofinku sun raba ku da Allahnku; zunubanku sun ɓoye fuskarsa daga gare ku, saboda kada yă ji.
nego su opačine vaše jaz otvorile između vas i Boga vašega. Vaši su grijesi lice njegovo zastrli, i on vas više ne sluša.
3 Gama hannuwanku sun ƙazantu da jini, yatsotsinku kuma da alhaki. Leɓunanku suna faɗin ƙarairayi, harshenku kuma yana raɗar mugayen abubuwa.
Jer ruke su vaše u krvi ogrezle, a vaši prsti u zločinima. Usne vam izgovaraju laž, a jezik podlost mrmlja.
4 Babu wani mai ce a yi adalci; babu wani mai nema a dubi al’amarinsa da mutunci. Sun dogara a gardandamin banza suna ƙarairayi; suna ɗaukar cikin ɓarna, su haifi mugunta.
Nitko s pravom tužbu ne podiže, niti koga sude po istini. U ništavilo se uzdaju, laž kazuju, začinju zloću, a rađaju bezakonje.
5 Suna ƙyanƙyashe ƙwan kāsā su kuma saƙa yanar gizo-gizo. Duk wanda ya ci ƙwansu zai mutu, kuma sa’ad da ƙwan ya fashe, zai ƙyanƙyashe kububuwa.
Legu jaja gujina, tkaju mrežu paukovu; pojede li tko njihovo jaje, umire, razbije li ga, iz njega ljutica izlazi.
6 Yanar gizo-gizonsu ba amfani don tufa; ba za su iya rufuwa da abin da suka yi ba. Ayyukansu mugaye ne, ayyukan tā da hargitsi kuma suna a hannuwansu.
Njihovim tkanjem nemoguće se odjenuti, ne možeš se pokriti njihovom rukotvorinom. Rukotvorine su njihove djela zločinačka, rukama svojim čine nasilje.
7 Ƙafafunsu sukan gaggauta zuwa aikata zunubi; suna da saurin zub da jini. Tunaninsu mugaye ne; lalaci da hallaka sun shata hanyoyinsu.
Noge njihove u zlo hitaju i brze su da krv nevinu proliju. Misli su im misli zločinačke, pustoš i propast na njinim su putima.
8 Ba su san hanyar salama ba; babu adalci a hanyoyinsu. Sun mai da su karkatattun hanyoyi; babu wanda zai yi tafiya a kansu ya sami salama.
Put mira oni ne poznaju, na stazama njihovim nema pravice. Iskrivili su svoje putove, tko njima kreće mira ne poznaje.
9 Saboda haka gaskiya ta yi nisa da mu, adalci kuma ba ya kaiwa gare mu. Muna neman haske, sai ga duhu; muna neman haske, sai muka yi ta tafiya cikin baƙin inuwa.
Stog' se pravo od nas udaljilo, zato pravda ne dopire do nas. Nadasmo se svjetlosti, a ono tama; i vidjelu, a ono u tmini hodimo.
10 Kamar makafi, sai lallubar bango muke yi, muna lallubawar hanyarmu kamar marasa idanu. Da tsakar rana muna tuntuɓe sai ka ce wuri ya fara duhu; cikin ƙarfafa, mun zama kamar matattu.
Pipamo kao slijepci duž zida, tapkamo kao bez očiju. Spotičemo se u podne k'o u sumraku, sasvim zdravi, kao da smo mrtvi.
11 Muna gurnani kamar beyar; muna ta ƙugi kamar kurciyoyi. Muna ta neman adalci amma ina; mun nemi fansa, amma yana can da nisa.
Svi mumljamo kao medvjedi i gučemo tužno kao golubovi. Očekivasmo Sud, a njega nema, i spasenje - od nas je daleko.
12 Gama laifofinmu suna da yawa a gabanka, zunubanmu kuma suna ba da shaida gāba da mu. Laifofinmu kullum suna a gabanmu, muna kuma sane da laifofinmu,
Jer mnogo je naših opačina pred tobom i grijesi naši protiv nas svjedoče. Doista, prijestupi su naši pred nama, mi znademo svoju krivicu;
13 tawaye da mūsun Ubangiji, mun juye bayanmu ga Allahnmu, zugawa a yi zalunci da tayarwa, faɗin ƙarairayi da zukatanmu suka shirya.
pobunili smo se i zanijekali Jahvu, odmetnuli se od Boga svojega, govorili podlo, odmetnički, mrmljali u srcu riječi lažljive.
14 Saboda haka aka kau da yin gaskiya adalci kuma ya tsaya can da nesa; gaskiya ta yi tuntuɓe a tituna, sahihanci ba zai shiga ba.
Tako je potisnuto pravo, i pravda mora stajati daleko. Jer na trgu posrnu istina i poštenju nema više pristupa.
15 Gaskiya ta ɓace gaba ɗaya, kuma duk wanda ya guji mugunta zai zama ganima. Ubangiji ya duba bai kuwa ji daɗi cewa babu adalci ba.
Vjernosti je ponestalo, a tko izbjegava zlo, bude opljačkan. Jahve vidje, i ne bi mu milo što nema pravice.
16 Ya ga cewa babu wani, ya yi mamaki cewa babu wanda zai shiga tsakani; saboda haka hannunsa ya aikata masa ceto, adalcinsa kuma ya raya shi.
Vidje da nema čovjeka, začudi se što nema posrednika. Tad mu pomože njegova mišica i njegova ga pravda poduprije.
17 Ya yafa sulke a matsayin rigar ƙirji, da hulan kwanon ceto a kansa; ya sa rigunan ɗaukar fansa ya kuma nannaɗe kansa da kishi kamar a cikin alkyabba.
Pravednost je obukao k'o oklop, stavio na glavu kacigu spasenja. Osvetom se odjenuo k'o haljom, ogrnu se revnošću kao plaštem.
18 Bisa ga abin da suka yi, haka za a sāka fushi a kan abokan gābansa ramuwa kuma a kan maƙiyansa; zai sāka wa tsibirai abin da ya dace da su.
Vratit će svakome po njegovim djelima: gnjev svojim protivnicima, odmazdu dušmanima.
19 Daga yamma, mutane za su ji tsoron Ubangiji, daga mafitar rana kuma, za su girmama ɗaukakarsa. Gama zai zo kamar rigyawa mai tsananin gudu cewa numfashin Ubangiji zai tafi tare da shi.
Sa zapada vidjet će ime Jahvino i Slavu njegovu s istoka sunčanog. Jer doći će kao uska rijeka koju goni dah Jahvin.
20 “Mai fansa zai zo Sihiyona, zuwa waɗanda suke cikin Yaƙub da suka tuba daga zunubansu,” in ji Ubangiji.
Ali doći će Otkupitelj Sionu, i onima od sinova Jakovljevih koji se obrate od svog otpadništva, riječ je Jahvina.
21 “Game da ni dai, ga alkawarina da su,” in ji Ubangiji. “Ruhuna, wanda yake a kanka, da kuma maganata da na sa a bakinka ba za tă rabu da bakinka ba, ko daga bakunan’ya’yanka ba, ko kuwa daga bakunan zuriyarsu ba daga wannan lokaci zuwa gaba da kuma har abada,” in ji Ubangiji.
“A ovo je moj Savez s njima,” govori Jahve. “Duh moj koji je na tebi i riječi moje koje stavih u tvoja usta neće izići iz usta tvojih ni usta tvojega potomstva, ni iz usta potomstva tvojih potomaka, od sada pa dovijeka,” veli Jahve.

< Ishaya 59 >