< Ishaya 54 >
1 “Ki rera, ya ke bakararriya, ke da ba ki taɓa haihuwa ba; ki ɓarke da waƙa, ki yi sowa don farin ciki, ke da ba ki taɓa naƙuda ba; domin’ya’yan mace mai kaɗaici sun fi na mai miji yawa,” in ji Ubangiji.
Fröjda dig, du ofruktsamma, du som intet föder; gläd dig med fröjd och berömmelse, du som intet hafvandes är; ty den ensamma hafver flera barn än den som man hafver, säger Herren.
2 “Ki fadada wurin tentinki, ki miƙe labulen tentinki da fāɗi, kada ki janye; ƙara tsawon igiyoyinta, ki kuma ƙara ƙarfin turakunta.
Förvidga din pauluns rum, och utsträck tapeten åt din tjäll; spar icke, förläng din tåg, och befäst dina pålar.
3 Gama za ki fadada zuwa dama da hagu; zuriyarki za su kori al’ummai su kuma zauna a kufan biranensu.
Ty du skall brista ut på högra sidon och den venstra, och din säd skall ärfa Hedningarna, och bo uti de förödda städer.
4 “Kada ki ji tsoro; ba za ki sha kunya ba. Kada ki ji tsoron wulaƙanci, ba za a ƙasƙantar da ke ba. Za ki manta da kunyar ƙuruciyarki ba kuwa za ki tuna da zargin zaman gwauruwarki ba.
Frukta dig intet; ty du skall icke till skam varda. Var icke blödig; ty du skall icke varda till blygd, utan du skall förgäta dins jungfrudoms blygd, och din enkodoms neso icke mer ihågkomma.
5 Gama Mahaliccinki shi ne mijinki, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ne Mai Fansarki; ana ce da shi Allahn dukan duniya.
Ty den dig gjort hafver, han är din man; Herren Zebaoth är hans Namn; och din förlossare, den Helige i Israel, den alla verldenes Gud kallad varder.
6 Ubangiji zai kira sai ka ce ke mace ce da aka yashe ta tana kuma damuwa a ranta, macen da ta yi aure a ƙuruciya, sai kawai aka ƙi ta,” in ji Allahnki.
Ty Herren hafver låtit dig vara uti det ryktet, att du äst såsom en öfvergifven och af hjertat bedröfvad qvinna, och såsom en ung hustru, den bortdrifven är, säger din Gud.
7 “Gama a ɗan ƙanƙanen lokaci na rabu da ke, amma da ƙauna mai zurfi zan sāke dawo da ke.
Jag hafver uti ett litet ögnablick öfvergifvit dig; men med stor barmhertighet vill jag församla dig.
8 Cikin fushi mai zafi na ɓoye fuskata daga gare ki na ɗan lokaci, amma da madawwamin alheri zan ji tausayinki,” in ji Ubangiji Mai Fansarki.
Jag hafver, uti vredenes ögnablick, som snarast gömt bort mitt ansigte för dig; men med eviga nåd vill jag förbarma mig öfver dig, säger Herren, din förlossare.
9 “A gare ni wannan ya yi kamar kwanakin Nuhu, sa’ad da na rantse cewa ruwan Nuhu ba za su ƙara rufe duniya ba. Yanzu fa na rantse ba zan yi fushi da ke ba, ba zan ƙara tsawata miki kuma ba.
Ty detta skall vara mig såsom Noahs flod; då jag svor, att Noahs flod icke mer skulle gå öfver jordena; alltså hafver jag svorit, att jag icke skall vredgas öfver dig, eller näpsa dig.
10 Ko da duwatsu za su girgiza a kuma tumɓuke tuddai, duk da haka madawwamiyar ƙaunata da nake yi miki ba za tă jijjigu ba ba kuwa za a kawar da alkawarin salamata ba,” in ji Ubangiji, wanda ya ji tausayinki.
Ty bergen skola väl vika, och högarna falla; men min nåd skall icke vika ifrå dig, och mins frids förbund skall icke förfalla, säger Herren, din förbarmare.
11 “Ya ke birni mai shan azaba, wadda hadari ya bulale ki ba a kuma ta’azantar da ke ba, zan gina ke da duwatsu turkuwoyis, zan kafa harsashenki da duwatsun saffaya.
Du elända, öfver hvilka alle väder gå, och du tröstlösa, si, jag vill lägga dina stenar såsom en prydning, och lägga din grundval med saphirer;
12 Zan gina hasumiyarki da jan yakutu, ƙofofinki kuma da duwatsu masu haske, dukan katangarki kuma da duwatsu masu daraja.
Och din fenster göra af christall, och dina portar af rubiner, och alla dina gränsor af utkorada stenar;
13 Ubangiji zai koya wa dukan’ya’yanki maza, da girma kuma salamar’ya’yanki zai zama.
Och all din barn lärd af Herranom, och stor frid dinom barnom.
14 Da adalci za a kafa ke. Zalunci zai yi nesa da ke; ba za ki kasance da wani abin da za ki ji tsoro ba. Za a kawar da duk wani abin banrazana; ba zai yi kusa da ke ba.
Du skall genom rättfärdighet beredd varda; du skall vara långt ifrån öfvervåld och orätt, så att du icke skall torfva frukta dig derföre; och ifrå förskräckelse, ty det skall icke nalkas dig.
15 In wani ya far miki, ba daga wurina ba ne; duk wanda ya far miki zai miƙa wuya gare ki.
Si, ho vill församla sig emot dig, och öfverfalla dig, då de församla sig utan mig?
16 “Duba, ni ne wanda na halicci maƙeri wanda yake zuga garwashi ya zama harshen wuta ya kuma ƙera makamin da ya dace da aikinsa. Ni ne kuma na halicci mai hallakarwa ya yi ɓarna;
Si, jag gör det, att smeden, som uppblås kolen i elden, han gör der ett tyg af, till sitt verk; ty jag gör ock, att förderfvaren förgås.
17 ba makamin da aka ƙera don yă cuce ki da zai yi nasara, za ki kuma mayar da magana ga duk wanda ya zarge ki. Wannan ne gādon bayin Ubangiji, kuma wannan ita ce nasararsu daga gare ni,” in ji Ubangiji.
Ty hvart och ett tyg, som emot dig tillredt varder, thy skall icke väl gå; och hvar och en tunga, som sig uppsätter emot dig, den skall du fördöma i dome. Detta är Herrans tjenares arf, och deras rättfärdighet af mig, säger Herren.