< Ishaya 53 >

1 Wa ya gaskata saƙonmu kuma ga wa hannun Ubangiji ya bayyana?
Mais, Seigneur, qui a cru à notre parole? A qui le bras du Seigneur a-t- il été révélé?
2 Ya yi girma kamar dashe marar ƙarfi, kamar saiwa kuma daga ƙeƙasasshiyar ƙasa. Ba shi da kyan gani ko wani makamin da zai ja hankalinmu, babu wani abin da yake da shi da zai sa mu yi sha’awarsa.
Nous l'avons annoncé, comme un petit enfant devant le Seigneur, comme une racine dans une terre altérée; il n'est point en lui de beauté ni de gloire; nous l'avons vu, et il n'avait ni éclat ni beauté.
3 Mutane suka rena shi suka ƙi shi, mutum ne cike da baƙin ciki, ya kuma saba da wahala. Kamar wanda mutane suna ɓuya fuskokinsu daga gare shi aka rena shi aka yi banza da shi.
Mais son aspect était méprisable, au-dessous de celui des fils des hommes. C'était un homme couvert de plaies, et sachant ce que c'est que la souffrance; car son visage était repoussant, sans honneur, et compté pour rien.
4 Tabbatacce ya ɗauki cututtukanmu ya kuma daure da baƙin cikinmu duk da haka muka ɗauka Allah ya hukunta shi ne, ya buge shi ya kuma sa ya sha azaba.
Il porte nos péchés, il souffre pour nous; et nous avons remarqué qu'il était dans la peine, dans la douleur, dans la torture.
5 Amma aka yi masa rauni saboda laifofinmu, aka ƙuje shi saboda kurakuranmu; hukuncin da ya kawo mana salama ya kasance a kansa, kuma ta wurin mikinsa ya sa muka warke.
Mais il avait été blessé pour nos péchés, il était brisé pour nos crimes; le châtiment qui devait nous rendre la paix est tombé sur lui; nous avons été guéris par ses meurtrissures.
6 Dukanmu, muna kama da tumakin da suka ɓata, kowannenmu ya kama hanyarsa; Ubangiji kuwa ya sa hukunci ya auko a kansa hukuncin da ya wajaba a kanmu.
Nous étions égarés comme des brebis; tout homme errait dans sa voie. Et le Seigneur l'a livré pour nos péchés;
7 Aka wulaƙanta shi aka kuma yi masa azaba, duk da haka bai buɗe bakinsa ba; aka kai shi kamar ɗan rago zuwa wurin yanka, kuma kamar tunkiya a gaban masu askinta tana shiru, haka bai buɗe bakinsa ba.
Et lui, si fort qu'on l'ait maltraité, il n'ouvre pas la bouche. Il a été conduit sous le couteau comme une brebis; et comme l'agneau muet devant le tondeur, ainsi il n'ouvre pas la bouche.
8 Da wulaƙanci da kuma hukunci aka ɗauke shi aka tafi. Wa kuwa zai yi maganar zuriyarsa? Gama an kawar da shi daga ƙasar masu rai; saboda laifin mutanena aka kashe shi.
Tout jugement lui a été enlevé en son humiliation. Qui racontera sa génération? car sa vie est effacée de la terre; il a été conduit à la mort à cause des péchés de mon peuple.
9 Aka yi jana’izarsa tare da mugaye, aka binne shi tare da masu arziki, ko da yake bai taɓa yin wani tashin hankali ba, ko a sami ƙarya a bakinsa.
Je donnerai les méchants pour prix de sa sépulture, et les riches pour prix de sa mort; parce qu'il n'a point commis de péchés, et que le mensonge n'a jamais été dans sa bouche.
10 Duk da haka nufin Ubangiji ne a ƙuje shi yă kuma sa yă sha wahala, kuma ko da yake Ubangiji ya sa ransa ya zama hadaya don zunubi, zai ga zuriyarsa zai kuma kawo masa tsawon rai, nufin Ubangiji kuma zai yi nasara a hannunsa.
Et il a plu au Seigneur de le purifier par l'effet de sa souffrance. Si vous faites une offrande, pour vos péchés, votre vie verra une postérité qui vivra longtemps. Et il a plu au Seigneur d'effacer
11 Bayan wahalar ransa, zai ga hasken rai, ya kuma gamsu; ta wurin saninsa bawana mai adalci zai’yantar da mutane masu yawa, zai kuma ɗauki laifofinsu.
Une part des douleurs de son âme, de lui montrer la lumière, de la former à l'intelligence, de justifier le Juste qui s'est sacrifié pour un grand nombre, et qui a porté leurs péchés.
12 Saboda haka zan ba shi rabo tare da manya, zai kuma raba ganima tare da masu ƙarfi, domin ya ba da ransa har mutuwa, aka kuma lissafta shi tare da masu laifofi. Gama ya ɗauki zunubin mutane masu yawa, ya kuma yi roƙo saboda laifofinsu.
C'est pourquoi il aura pour héritage une grande multitude; il partagera les dépouilles des forts, en récompense de ce que sa vie aura été livrée au supplice, qu'il aura été regardé comme un pécheur, qu'il aura porté sur lui les péchés de beaucoup d'hommes, et que, pour leurs iniquités, il aura été livré à la mort.

< Ishaya 53 >