< Ishaya 46 >

1 Bel ya rusuna, Nebo ya durƙusa ƙasa; ana ɗaukan gumakansu a kan dabbobi ne. Siffofin da ake yawo da su nawaya ne, kayan nauyi masu gajiyarwa.
Bel is bowed downe: Nebo is fallen: their idoles were vpon the beastes, and vpon the cattell: they which did beare you, were laden with a wearie burden.
2 Sun durƙusa suka kuma rusuna tare; ba su iya kuɓutar da nauyin kaya su kansu sukan tafi bauta.
They are bowed downe, and fallen together: for they coulde not rid them of the burden, and their soule is gone into captiuitie.
3 “Ku kasa kunne gare ni, ya ku gidan Yaƙub, dukanku waɗanda kuka rage na gidan Isra’ila, ku da na lura da ku tun da aka yi cikinku, na kuma riƙe ku tun haihuwarku.
Heare ye me, O house of Iaakob, and all that remaine of the house of Israel, which are borne of me from the wombe, and brought vp of me from the birth.
4 Har lokacin da kuka tsufa kuka yi furfura ni ne shi, ni ne shi wanda zai lura da ku. Na yi ku zan kuma riƙe ku; zan lura da ku in kuma kuɓutar da ku.
Therefore vnto olde age, I the same, euen I will beare you vntill the hoare heares: I haue made you: I will also beare you, and I will cary you and I will deliuer you.
5 “Da wa za ku kwatanta ni ko ku ɗauka daidai da ni? Da wa nake kama da har da za ku kwatanta ni?
To whom will ye make me like or make me equall, or copare me, that I should be like him?
6 Waɗansu sukan zubar da zinariya daga jaka su kuma auna azurfa a ma’auni; sukan yi haya maƙerin zinariya don yă ƙera allah, su kuma rusuna su yi masa sujada.
They draw gold out of the bagge and weigh siluer in the balance, and hire a goldsmith to make a god of it, and they bowe downe, and worship it.
7 Sukan daga shi a kafaɗunsu su kuma ɗauke shi; sukan kafa shi a tsaye a wurinsa, a can kuwa zai tsaya. Daga wannan wuri ba zai iya gusawa ba. Ko da wani ya nemi taimakonsa, ba ya amsawa; ba zai iya cetonsa daga wahala ba.
They beare it vpon the shoulders: they carie him and set him in his place: so doeth he stand, and cannot remoue from his place. Though one crie vnto him, yet can he not answere, nor deliuer him out of his tribulation.
8 “Ku tuna da wannan, ku sa shi a zuciya, ku riƙe shi a zuciya, ku’yan tawaye.
Remember this, and be ashamed: bring it againe to minde, O you transgressers.
9 Ku tuna da abubuwan da suka riga suka faru, waɗannan na tun dā; ni ne Allah, kuma babu wani; ni ne Allah kuma babu wani kamar ni.
Remember the former things of old: for I am God, and there is none other God, and there is nothing like me,
10 Nakan sanar da ƙarshe tun daga farko, daga fil azal, abin da yake zuwa nan gaba. Na ce nufina zai tabbata, kuma zan aikata dukan abin da na gan dama.
Which declare the last thing from the beginning: and from of olde, the things that were not done, saying, My counsell shall stand, and I will doe whatsoeuer I will.
11 Daga gabas na kira tsuntsun da yake farauta; daga can ƙasa mai nesa, wani mutumin da zai cika nufina. Abin da na riga na faɗa, shi zan sa ya faru; abin da na shirya, shi zan aikata.
I call a birde from the East, and the man of my counsell from farre: as I haue spoken, so will I bring it to passe: I haue purposed it, and I will doe it.
12 Ku kasa kunne, ku masu taurinkai, ku da kuke nesa da adalci.
Heare me, ye stubburne hearted, that are farre from iustice.
13 Ina kawo adalcina kusa, ba shi da nisa; kuma cetona ba zai jinkirta ba. Zan yi wa Sihiyona ceto, darajata ga Isra’ila.
I bring neere my iustice: it shall not be farre off, and my saluation shall not tarie: for I wil giue saluation in Zion, and my glory vnto Israel.

< Ishaya 46 >