< Ishaya 44 >

1 “Amma yanzu ka saurara, ya Yaƙub, bawana, Isra’ila, wanda zaɓa.
“Şimdi, ey kulum Yakup soyu, Seçtiğim İsrail halkı, dinle!
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi wanda ya yi ka, wanda ya siffanta ka a cikin mahaifa, wanda kuma zai taimake ka. Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub, bawana, Yeshurun, wanda na zaɓa.
Seni yaratan, rahimde sana biçim veren, Sana yardım edecek olan RAB şöyle diyor: ‘Korkma, ey kulum Yakup soyu, Ey seçtiğim Yeşurun!
3 Gama zan zuba ruwa a ƙeƙasasshiyar ƙasa, rafuffuka kuma a busasshiyar ƙasa; zan ba da Ruhuna ga’ya’yanka, albarkata kuma ga zuriyarka.
“‘Susamış toprağı sulayacak, Kurumuş toprakta dereler akıtacağım. Çocuklarının üzerine Ruhum'u dökecek, Soyunu kutsayacağım.
4 Za su tsiro kamar ciyawa a wuriyar ruwa, kamar kurmi kusa da rafuffuka masu gudu.
Akarsu kıyısında otlar arasında yükselen Kavaklar gibi boy atacaklar.’
5 Wani zai ce, ‘Ni na Ubangiji ne’; wani kuma zai kira kansa da sunan Yaƙub; har yanzu wani zai rubuta a hannunsa, ‘Na Ubangiji,’ ya kuma ɗauki sunan Isra’ila.
“Kimi, ‘Ben RAB'be aitim’ diyecek, Kimi Yakup adını alacak, Kimi de eline ‘RAB'be ait’ yazıp İsrail adını benimseyecek.”
6 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, Sarki da kuma Mai Fansar Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki. Ni ne farko ni ne kuma ƙarshe; in ban da ni babu wani Allah.
RAB, İsrail'in Kralı ve Kurtarıcısı, Her Şeye Egemen RAB diyor ki, “İlk ve son benim, Benden başka Tanrı yoktur.
7 Wane ne kuwa kama da ni? Ya faɗa a ji. Bari yă yi shela ya kuma nuna shi a gabana mene ne ya faru tun da na kafa mutanena na dā, mene ne kuma bai riga ya faru ba, I, bari yă faɗa abin da zai zo.
Benim gibi olan var mı? Haber versin. Ezeli halkımı var ettiğimden beri olup bitenleri, Bundan sonra olacakları söyleyip sıralasın, Evet, gelecek olayları bildirsin!
8 Kada ku firgita kada kuma ku ji tsoro. Ban furta wannan na kuma yi faɗar haka tuntuni ba? Ku ne shaiduna. Akwai wani Allah in ban da ni? A’a, babu wani Dutse; ban san da wani ba.”
Yılmayın, korkmayın! Size çok önceden beri söyleyip açıklamadım mı? Tanıklarım sizsiniz. Benden başka Tanrı var mı? Hayır, başka Kaya yok; Ben bir başkasını bilmiyorum.”
9 Duk masu yin gumaka ba kome ba ne, da kuma abubuwan da suke ɗauka da daraja banza ne. Waɗanda za su yi magana a madadinsu makafi ne; jahilai ne, marasa kunya.
Putlara biçim verenlerin hepsi boş insanlardır. Değer verdikleri nesneler hiçbir işe yaramaz. Putların tanıkları onlardır; Ne bir şey görür ne de bir şey bilirler. Bunun sonucunda utanç içinde kalacaklar.
10 Waɗanda suke siffanta allah su kuma yi zubin gunki, waɗanda ba za su yi musu ribar kome ba?
Kim yararsız ilaha biçim vermek, Dökme put yapmak ister?
11 Shi da irinsa za su sha kunya; masu sassaƙa ba kome ba mutane ne kurum. Bari su tattaru su ɗauki matsayinsu; za su firgita su kuma sha mummunan kunya.
Bakın, bu putlarla uğraşanların hepsi utanacak. Onları yapanlar salt insan. Hepsi toplanıp yargılanmaya gelsin. Dehşete düşecek, utanacaklar birlikte.
12 Maƙeri yakan ɗauki kayan aiki ya yi aiki da shi a cikin garwashi; ya ƙera gunki da guduma, ya gyara shi da hannuwansa masu ƙarfi. Yakan ji yunwa ya kuma rasa ƙarfi; yakan sha ruwa ya kuma ji gajiya.
Demirci aletini alır, Kömür ateşinde çalışır, Çekiçle demire biçim verir. Güçlü koluyla onu işler. Acıkır, güçsüz kalır, su içmeyince tükenir.
13 Kafinta yakan gwada katako yă kuma zāna siffar da alli; yă goge shi da kayan aiki yă kuma zāna shi da alƙalami. Yă siffanta shi a kamannin mutum, mutum cikin dukan darajarsa, don yă ajiye shi a cikin masujada.
Marangoz iple ölçü alır, Tahtayı tebeşirle çizer. Raspayla tahtayı biçimlendirir, Pergelle işaretler, insan biçimi verir. İnsan güzelliğinde, Evde duracak bir put yapar.
14 Yakan ka da itacen saifires, ko kuwa ya ɗauki saifires ko oak. Yă bar shi yă yi girma a cikin itatuwan kurmi, ko yă shuka itacen fir, ruwan sama kuma yă sa yă yi girma.
İnsan kendisi için sedir ağaçları keser, Palamut, meşe ağaçları alır. Ormanda kendine bir ağaç seçer. Bir çam diker, ama ağacı büyüten yağmurdur.
15 Abin hura wutar mutum ne; yakan ɗebi waɗansu yă hura wuta don yă ji ɗumi, ya hura wuta yă gasa burodi. Amma yakan ƙera zinariya yă kuma yi masa sujada; yakan yi gunki sa’an nan yă rusuna masa.
Sonra ağaç odun olarak kullanılır. İnsan aldığı odunla hem ısınır, Hem tutuşturup ekmek pişirir, Hem de bir ilah yapıp tapınır. Yaptığı putun önünde yere kapanır.
16 Rabin katakon yakan ƙone a wuta; a kansa yakan dafa abincinsa, yă gasa namansa yă kuma ci sai ya ƙoshi. Yakan ji ɗumi yă kuma ce, “Aha! Na ji ɗumi; na gan wutar.”
Odunun bir kısmını yakar, Ateşinde et kızartıp karnını doyurur. Isınınca bir oh çeker, “Isındım, ateşin sıcaklığını duyuyorum” der.
17 Da sauran itacen yakan yi allah, gunkinsa; yă rusuna masa yă kuma yi sujada. Yakan yi masa addu’a yă ce, “Ka cece ni; kai ne allahna.”
Artakalan odundan kendine bir ilah, Oyma put yapar; Önünde yere kapanıp ona tapınır, “Beni kurtar, çünkü ilahım sensin” diye yakarır.
18 Ba su san kome ba, ba su fahimci kome ba; an rufe idanunsu don kada su gani, tunaninsu kuma a rufe don kada su fahimta.
Böyleleri anlamaz, bilmez. Çünkü gözleri de zihinleri de öylesine kapalı ki, Görmez, anlamazlar.
19 Ba wanda yakan dakata ya yi tunani, ba wanda yake da sani ko fahimi ya ce, “Da rabinsa na yi amfani da shi don hura wuta; na ma gasa burodi a kan garwashinsa, na gasa nama na kuma ci. Ya kamata in yi abin ƙyama daga abin da ya rage? Ya kamata in rusuna wa guntun katako?”
Durup düşünmez, bilmez, Anlamazlar ki şöyle desinler: “Odunun bir kısmını yakıp Ateşinde ekmek pişirdim, et kızartıp yedim. Artakalanından iğrenç bir şey mi yapayım? Bir odun parçasının önünde yere mi kapanayım?”
20 Yana cin toka, zuciyar da ta ruɗe tana ɓad da shi; ba zai iya cece kansa ba, ko ya ce, “Wannan abin da yake hannun dama na ba ƙarya ba ne?”
Külle besleniyorlar. Aldanan yürekleri onları saptırıyor. Canlarını kurtaramaz, “Sağ elimdeki şu nesne aldatıcı değil mi?” diyemezler.
21 “Tuna da waɗannan abubuwa, ya Yaƙub, gama kai bawana ne, ya Isra’ila. Na yi ka, kai bawana ne; Ya Isra’ila, ba zan manta da kai ba.
“Ey Yakup soyu, ey İsrail, Söylediklerimi anımsayın, çünkü kulumsunuz. Size ben biçim verdim, kulumsunuz; Seni unutmam, ey İsrail.
22 Na shafe laifofinka kamar girgije, zunubanka kamar hazon safe. Ka komo wurina, gama na kuɓutar da kai.”
İsyanlarınızı bulut gibi, Günahlarınızı sis gibi sildim. Bana dönün, çünkü sizi kurtardım.”
23 Ku rera don farin ciki, ya sammai, gama Ubangiji ya aikata wannan; ku yi sowa, ya duniya a ƙarƙashi. Ku ɓarke da waƙoƙi, ku duwatsu, ku jeji da dukan itatuwanku, gama Ubangiji ya kuɓutar da Yaƙub, ya nuna ɗaukakarsa a cikin Isra’ila.
Sevinçle haykırın, ey gökler, Çünkü bunu RAB yaptı. Haykırın, ey yerin derinlikleri. Ey dağlar, ey orman, ormandaki her ağaç, Sevinç çığlıklarına katılın. Çünkü RAB Yakup soyunu kurtararak İsrail'de görkemini gösterdi.
24 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarka, wanda ya yi ka a cikin mahaifa. “Ni ne Ubangiji, wanda ya yi dukan abubuwa, wanda ya shimfiɗa sammai ya kuma kafa harsashen duniya da kansa,
Sizi kurtaran, Size rahimde biçim veren RAB diyor ki, “Her şeyi yaratan, Gökleri yalnız başına geren, Yeryüzünü tek başına seren, Sahte peygamberlerin belirtilerini boşa çıkaran, Falcılarla alay eden, Bilgeleri geri çeviren, Bilgilerini saçmalığa dönüştüren, Kulunun sözlerini yerine getiren, Ulaklarının peygamberlik sözlerini gerçekleştiren, Yeruşalim için, ‘İçinde oturulacak’, Yahuda kentleri için, ‘Yeniden kurulacak, Yıkıntılarını onaracağım’ diyen; Engine, ‘Kuru! Sularını kurutacağım’ diyen, Koreş için, ‘O çobanımdır, Her istediğimi yerine getirecek’, Yeruşalim için, ‘Yeniden kurulacak’, Tapınak için, ‘Temeli atılacak’ diyen RAB benim.”
25 wanda ya sassāke alamun annabawan ƙarya ya masu duba suka zama wawaye, wanda ya tumɓuke koyon masu hikima ya mai da shi banza,
26 wanda ya tabbatar da maganganun bayinsa ya kuma cika annabce-annabcen’yan aikansa, “wanda ya ce game da Urushalima, ‘Za a zauna a cikinta,’ game da garuruwan Yahuda, ‘Za a gina su,’
27 wanda ya ce wa zurfin ruwaye, ‘Ku bushe, zan kuma busar da rafuffukanku,’
28 wanda ya yi zancen Sairus ya ce, ‘Shi ne makiyayina zan kuma cika dukan abin da na gan dama; zai yi zancen Urushalima cewa, “Bari a sāke gina ta,” game da haikali kuma cewa, “Bari a kafa harsashinsa.”’

< Ishaya 44 >