< Ishaya 41 >

1 “Ku yi shiru a gabana, ku tsibirai! Bari al’ummai su sabunta ƙarfinsu! Bari su zo gaba su yi magana; bari mu sadu a wurin shari’a.
RAB diyor ki, “Susun karşımda, ey kıyı halkları! Halklar güçlerini tazelesin, Öne çıkıp konuşsunlar. Yargı için bir araya gelelim.
2 “Wa ya zuga wannan daga gabas, yana kiransa cikin adalci ga yin hidima? Ya miƙa masa al’ummai ya kuma yi nasara da sarakuna a gabansa. Ya mai da su ƙura da takobinsa, zuwa inda iska ke hurawa ta wurin bugun da ya yi musu.
“Doğudan adaleti harekete geçiren, Hizmete koşan kim? Ulusları önüne katıyor, krallara baş eğdiriyor. Kılıcıyla toz ediyor onları, Yayıyla savrulan samana çeviriyor.
3 Ya fafare su ya kuma yi tafiyarsa lafiya ƙalau, a hanyar da ƙafafunsa ba su taɓa bi ba.
Kovalıyor onları, Ayak basmadığı bir yoldan esenlikle geçiyor.
4 Wane ne ya taɓa yin haka ya kuma sa ya faru, yana kira ga tsararraki daga farko? Ni, Ubangiji ina can tun farkonsu ni kuma ina can har ƙarshe, Ni ne shi.”
Bunları yapıp gerçekleştiren, Kuşakları başlangıçtan beri çağıran kim? Ben RAB, ilkim; sonuncularla da yine Ben olacağım.”
5 Tsibirai sun gan shi suka kuma ji tsoro; iyakokin duniya sun yi rawar jiki. Suka kusato suka kuma zo gaba;
Kıyı halkları bunu görüp korktu. Dünyanın dört bucağı titriyor. Yaklaşıyor, geliyorlar.
6 kowa na taimakon wani yana ce wa ɗan’uwansa, “Ka ƙarfafa!”
Herkes komşusuna yardım ediyor, Kardeşine, “Güçlü ol” diyor.
7 Masassaƙi yakan ƙarfafa maƙerin zinariya, kuma shi mai gyara da guduma ya yi sumul yakan ƙarfafa mai harhaɗawa. Ya ce game da haɗin, “Ya yi kyau.” Yakan buga ƙusoshi su riƙe gunkin don kada yă fāɗi.
Zanaatçı kuyumcuyu yüreklendiriyor, Madeni çekiçle düzleyen, “Lehim iyi oldu” diyerek örse vuranı yüreklendiriyor. Kımıldamasın diye putu yerine çiviliyor.
8 “Amma kai, ya Isra’ila, bawana, Yaƙub, wanda na zaɓa, zuriyar Ibrahim abokina,
“Ama sen, ey kulum İsrail, Seçtiğim Yakup soyu, Dostum İbrahim'in torunları!
9 na ɗauke ka daga iyakar duniya, daga kusurwoyi masu nesa na kira ka. Na ce, ‘Kai bawana ne’; na zaɓe ka ban kuwa ƙi ka ba.
Sizleri dünyanın dört bucağından topladım, En uzak yerlerden çağırdım. Dedim ki, ‘Sen kulumsun, seni seçtim, Seni reddetmedim.’
10 Saboda haka kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai; kada ka karai, gama ni ne Allahnka. Zan ƙarfafa ka in kuma taimake ka; zan riƙe ka da hannun damana mai adalci.
Korkma, çünkü ben seninleyim, Yılma, çünkü Tanrın benim. Seni güçlendireceğim, evet, sana yardım edeceğim; Zafer kazanan sağ elimle sana destek olacağım.
11 “Duk wanda ya yi fushi da kai tabbatacce zai sha kunya da ƙasƙanci; waɗanda suka yi hamayya da kai za su zama kamar ba kome ba su kuma hallaka.
“Sana öfkelenenlerin hepsi utanacak, rezil olacak. Sana karşı çıkanlar hiçe sayılıp yok olacak.
12 Ko ka nemi abokan gābanka, ba za ka same su ba. Waɗanda suke yaƙi da kai za su zama kamar ba kome ba.
Seninle çekişenleri arasan da bulamayacaksın. Seninle savaşanlar hiçten beter olacak.
13 Gama ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya riƙe ka da hannun damana ya kuma ce maka, Kada ka ji tsoro; zan taimake ka.
Çünkü sağ elinden tutan, ‘Korkma, sana yardım edeceğim’ diyen Tanrın RAB benim.
14 Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub marar ƙarfi, ya ƙaramin Isra’ila, gama ni kaina zan taimake ka,” in ji Ubangiji, Mai Fansarka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
“Ey Yakup soyu, toprak kurdu, Ey İsrail halkı, korkma! Sana yardım edeceğim” diyor RAB, Seni kurtaran İsrail'in Kutsalı.
15 “Duba, zan sa ka cikin abin sussuka, saboda kuma mai kaifi mai haƙora da yawa. Za ka yi sussukar duwatsu ka ragargaza su, ka kuma farfashe tuddai su zama kamar yayi.
“İşte, seni dişli, keskin, yepyeni bir harman düveni yaptım. Harman edip ufalayacaksın dağları, Tepeleri samana çevireceksin.
16 Za ka tankaɗe su, iska kuma ta kwashe su, guguwa kuma za tă warwatsa su. Amma za ka yi farin ciki a cikin Ubangiji ka kuma ɗaukaka a cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Onları savurduğunda rüzgar alıp götürecek, Darmadağın edecek hepsini kasırga. Sense RAB'de sevinç bulacak, İsrail'in Kutsalı'yla övüneceksin.
17 “Matalauta da mabukata suna neman ruwa, amma babu kome; harsunansu sun bushe saboda ƙishi. Amma Ni Ubangiji zan amsa musu; Ni, Allah na Isra’ila, ba zan yashe su ba.
“Düşkünlerle yoksullar su arıyor, ama yok. Dilleri kurumuş susuzluktan. Ben RAB, onları yanıtlayacağım, Ben, İsrail'in Tanrısı, onları bırakmayacağım.
18 Zan sa koguna su malalo a ƙeƙasassun tuddai, maɓulɓulan ruwa kuma a kwaruruka. Zan mai da hamada tafkunan ruwa, busasshiyar ƙasa kuma ta zama maɓulɓulan ruwa.
Çıplak tepeler üzerinde ırmaklar, Vadilerde su kaynakları yapacağım. Çölü havuza, Kurak toprağı pınara çevireceğim.
19 Zan sa a hamada ta tsiro da al’ul da itacen ƙirya, da itacen ci-zaƙi, da zaitun. Zan sa itace mai girma a ƙasashe masu sanyi ya tsiro a ƙeƙasasshiyar ƙasa, tare da fir da kuma saifires,
Çölü sedir, akasya, Mersin ve iğde ağaçlarına kavuşturacağım. Bozkıra çam, köknar Ve selviyi bir arada dikeceğim.
20 don mutane su gani su kuma sani, su lura su kuma fahimci, cewa hannun Ubangiji ne ya aikata haka, cewa Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya sa abin ya faru.
Öyle ki, insanlar görüp bilsinler, Hep birlikte düşünüp anlasınlar ki, Bütün bunları RAB'bin eli yapmış, İsrail'in Kutsalı yaratmıştır.”
21 “Ka gabatar da damuwarka,” in ji Ubangiji. “Ka kawo gardandaminka,” in ji Sarki na Yaƙub.
“Davanızı sunun” diyor RAB, “Kanıtlarınızı ortaya koyun” diyor Yakup'un Kralı,
22 “Ka shigar da gumakanka don su faɗa mana abin da zai faru. Faɗa mana abubuwan da suka riga suka faru, domin mu lura da su mu kuma san abin da zai faru a ƙarshe. Ko kuwa ku furta mana abubuwan da za su faru,
“Putlarınızı getirin de olacakları bildirsinler bize. Olup bitenleri bildirsinler ki düşünelim, Sonuçlarını bilelim. Ya da gelecekte olacakları duyursunlar bize.
23 faɗa mana abin da nan gaba ta ƙunsa, don mu san cewa ku alloli ne. Ku yi wani abu, mai kyau ko mummuna, don mu ji tsoro da fargaba.
Ey putlar, bundan sonra olacakları bize bildirin de, İlah olduğunuzu bilelim! Haydi bir iyilik ya da kötülük edin de, Hepimiz korkup dehşete düşelim.
24 Amma ku ba kome ba ne kuma ayyukanku banza da wofi ne; duk wanda ya zaɓe ku abin ƙyama ne.
Siz de yaptıklarınız da hiçten betersiniz, Sizi yeğleyen iğrençtir.
25 “Na zuga wani daga arewa, ya kuwa zo, wani daga inda rana ke fitowa wanda yake kira bisa sunana. Yana takawa a kan masu mulki kamar da taɓarya, sai ka ce maginin tukwane yana taka laka.
“Kuzeyden birini harekete geçirdim, geliyor, Gün doğusundan beni adımla çağıran biri. Çömlekçinin balçığı çiğnediği gibi, Önderleri çamur gibi çiğneyecek ayağıyla.
26 Wa ya faɗi wannan tun daga farko, don mu sani, ko kafin ya faru, don mu ce, ‘Ya faɗi daidai’? Ba wanda ya faɗa wannan, ba wanda ya riga faɗe shi, ba wanda ya ji wata magana daga gare ku.
Hanginiz bunu başlangıçtan bildirdi ki, bilelim, Kim önceden bildirdi ki, ‘Haklısın’ diyelim? Konuştuğunuzu bildiren de Duyuran da Duyan da olmadı hiç.
27 Ni ne na farkon da ya ce wa Sihiyona, ‘Duba, ga su nan!’ Na ba wa Urushalima saƙon labari mai daɗi.
Siyon'a ilk, ‘İşte, geldiler’ diyen benim. Yeruşalim'e müjdeci gönderdim.
28 Na duba amma ba kowa ba wani a cikinsu da zai ba da shawara, ba wani da zai ba da amsa sa’ad da na tambaye su.
Bakıyorum, aralarında öğüt verebilecek kimse yok ki, Onlara danışayım, onlar da yanıtlasınlar.
29 Duba, dukansu masu ƙarya ne! Ayyukansu ba su da riba; siffofinsu iska ne kawai da ruɗami.
Hepsi bomboş, yaptıkları da bir hiç. Halkın putları yalnızca yeldir, sıfırdır.”

< Ishaya 41 >