< Ishaya 41 >
1 “Ku yi shiru a gabana, ku tsibirai! Bari al’ummai su sabunta ƙarfinsu! Bari su zo gaba su yi magana; bari mu sadu a wurin shari’a.
Listen to me in silence, you people who live in lands beyond the sea. Let the nations regain their strength. Then let them come and speak, and let us join together for judgment.
2 “Wa ya zuga wannan daga gabas, yana kiransa cikin adalci ga yin hidima? Ya miƙa masa al’ummai ya kuma yi nasara da sarakuna a gabansa. Ya mai da su ƙura da takobinsa, zuwa inda iska ke hurawa ta wurin bugun da ya yi musu.
Who has encouraged this one from the east who is called into God's service to do what is right? He gives him nations, and helps him trample kings underfoot. He makes them like dust with his sword, and turns them into chaff with his bow, blown before him on the wind.
3 Ya fafare su ya kuma yi tafiyarsa lafiya ƙalau, a hanyar da ƙafafunsa ba su taɓa bi ba.
He chases them down, and goes on unharmed, not following the usual routes.
4 Wane ne ya taɓa yin haka ya kuma sa ya faru, yana kira ga tsararraki daga farko? Ni, Ubangiji ina can tun farkonsu ni kuma ina can har ƙarshe, Ni ne shi.”
Who has achieved and done this, calling into existence each generation from the beginning of time? I, the Lord, the first and the last, I am the one.
5 Tsibirai sun gan shi suka kuma ji tsoro; iyakokin duniya sun yi rawar jiki. Suka kusato suka kuma zo gaba;
The islands watch in fear, the distant lands tremble. They get together and consult.
6 kowa na taimakon wani yana ce wa ɗan’uwansa, “Ka ƙarfafa!”
They all help each other, encouraging one another to “Be strong!”
7 Masassaƙi yakan ƙarfafa maƙerin zinariya, kuma shi mai gyara da guduma ya yi sumul yakan ƙarfafa mai harhaɗawa. Ya ce game da haɗin, “Ya yi kyau.” Yakan buga ƙusoshi su riƙe gunkin don kada yă fāɗi.
The craftsman encourages the goldsmith; the one who beats out the metal with a hammer encourages the one hitting the anvil, saying the soldering is good. They nail the idol down so it won't fall over.
8 “Amma kai, ya Isra’ila, bawana, Yaƙub, wanda na zaɓa, zuriyar Ibrahim abokina,
But you, Israel, my servant, Jacob, the ones I have chosen, descendants of my friend Abraham,
9 na ɗauke ka daga iyakar duniya, daga kusurwoyi masu nesa na kira ka. Na ce, ‘Kai bawana ne’; na zaɓe ka ban kuwa ƙi ka ba.
I brought you back from distant lands, I called you back from faraway places, telling you, “You are my servants.” I have chosen you, and I have not abandoned you.
10 Saboda haka kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai; kada ka karai, gama ni ne Allahnka. Zan ƙarfafa ka in kuma taimake ka; zan riƙe ka da hannun damana mai adalci.
Don't be afraid, for I am with you! Don't be frightened for I, your God, will make you strong, and I will certainly help you. I will support you with my strong hand, acting for what is right.
11 “Duk wanda ya yi fushi da kai tabbatacce zai sha kunya da ƙasƙanci; waɗanda suka yi hamayya da kai za su zama kamar ba kome ba su kuma hallaka.
See—everyone who is angry with you will be ashamed and disgraced. Those who fight against you will end up as nothing and die.
12 Ko ka nemi abokan gābanka, ba za ka same su ba. Waɗanda suke yaƙi da kai za su zama kamar ba kome ba.
Even though you look for your enemies, you won't find them. Those who attack you will become absolutely nothing.
13 Gama ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya riƙe ka da hannun damana ya kuma ce maka, Kada ka ji tsoro; zan taimake ka.
For I the Lord will grab you by the hand and tell you, “Don't be afraid! I myself will help you.
14 Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub marar ƙarfi, ya ƙaramin Isra’ila, gama ni kaina zan taimake ka,” in ji Ubangiji, Mai Fansarka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Don't be frightened, Jacob, you little worm, you people of Israel, for I will help you,” declared the Lord your Savior, the Holy One of Israel.
15 “Duba, zan sa ka cikin abin sussuka, saboda kuma mai kaifi mai haƙora da yawa. Za ka yi sussukar duwatsu ka ragargaza su, ka kuma farfashe tuddai su zama kamar yayi.
Look! I will make you into a new and sharp threshing device, with many pointed teeth. You will thresh the mountains and crush the hills, turning them into chaff.
16 Za ka tankaɗe su, iska kuma ta kwashe su, guguwa kuma za tă warwatsa su. Amma za ka yi farin ciki a cikin Ubangiji ka kuma ɗaukaka a cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
You will throw them into the air, the wind will carry them away, and a storm will scatter them. Then you will be happy in the Lord, and boast about the Holy One of Israel.
17 “Matalauta da mabukata suna neman ruwa, amma babu kome; harsunansu sun bushe saboda ƙishi. Amma Ni Ubangiji zan amsa musu; Ni, Allah na Isra’ila, ba zan yashe su ba.
The poor and needy search for water, but don't find any—their tongues are dry with thirst. I, the Lord, will respond to them; I, the God of Israel, won't abandon them.
18 Zan sa koguna su malalo a ƙeƙasassun tuddai, maɓulɓulan ruwa kuma a kwaruruka. Zan mai da hamada tafkunan ruwa, busasshiyar ƙasa kuma ta zama maɓulɓulan ruwa.
I will open up rivers in the desolate highlands and springs in the valleys. I will make pools in the wilderness and springs in the desert.
19 Zan sa a hamada ta tsiro da al’ul da itacen ƙirya, da itacen ci-zaƙi, da zaitun. Zan sa itace mai girma a ƙasashe masu sanyi ya tsiro a ƙeƙasasshiyar ƙasa, tare da fir da kuma saifires,
I will plant cedars, acacias, myrtles, and olive trees in the desert. I will place evergreens in the desert, firs and box trees together.
20 don mutane su gani su kuma sani, su lura su kuma fahimci, cewa hannun Ubangiji ne ya aikata haka, cewa Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya sa abin ya faru.
In this way everyone can see and know, they can think about it and draw the conclusion that the it is the Lord who has done this, that the Holy One of Israel made it happen.
21 “Ka gabatar da damuwarka,” in ji Ubangiji. “Ka kawo gardandaminka,” in ji Sarki na Yaƙub.
“Now you submit your case,” says the Lord. “Present your evidence,” says the King of Jacob.
22 “Ka shigar da gumakanka don su faɗa mana abin da zai faru. Faɗa mana abubuwan da suka riga suka faru, domin mu lura da su mu kuma san abin da zai faru a ƙarshe. Ko kuwa ku furta mana abubuwan da za su faru,
“Let them come and tell us what's about to happen. Let them explain the things of the past, so that we can think about them and discover the final outcome. Or they can tell us about the future.
23 faɗa mana abin da nan gaba ta ƙunsa, don mu san cewa ku alloli ne. Ku yi wani abu, mai kyau ko mummuna, don mu ji tsoro da fargaba.
Predict what's coming so we can know for sure that you are gods. At least do something, good or bad, to impress us when we see it.
24 Amma ku ba kome ba ne kuma ayyukanku banza da wofi ne; duk wanda ya zaɓe ku abin ƙyama ne.
But look at you! You're nothing, and you can't do anything! Anyone who chooses you is disgusting!
25 “Na zuga wani daga arewa, ya kuwa zo, wani daga inda rana ke fitowa wanda yake kira bisa sunana. Yana takawa a kan masu mulki kamar da taɓarya, sai ka ce maginin tukwane yana taka laka.
I have encouraged the one who comes from the north. He is from the east, and will respect me. He will tread on rulers as if they were mortar, like a potter treading on clay.
26 Wa ya faɗi wannan tun daga farko, don mu sani, ko kafin ya faru, don mu ce, ‘Ya faɗi daidai’? Ba wanda ya faɗa wannan, ba wanda ya riga faɗe shi, ba wanda ya ji wata magana daga gare ku.
Who announced this beforehand so that we could know about it? Who let us know in the past, so that now we could say: ‘He was right’? None of you announced it, none of you predicted it, and nobody heard you say a word!
27 Ni ne na farkon da ya ce wa Sihiyona, ‘Duba, ga su nan!’ Na ba wa Urushalima saƙon labari mai daɗi.
I was the first to announce to Zion: ‘Look, here they are!’ I was the one who brought to Jerusalem the good news.
28 Na duba amma ba kowa ba wani a cikinsu da zai ba da shawara, ba wani da zai ba da amsa sa’ad da na tambaye su.
I look at these idols, and find there is no one who can say anything. None of them can give advice; when I ask them something, they can't even answer.
29 Duba, dukansu masu ƙarya ne! Ayyukansu ba su da riba; siffofinsu iska ne kawai da ruɗami.
Look at them! They're all evil, deceptive things. They can't do anything! They're just idols full of hot air!”