< Ishaya 4 >

1 A wannan rana mata guda bakwai za su cafke namiji guda su ce, “Ma ciyar da kanmu mu kuma yi wa kanmu sutura; ka dai bari mu ce kai ne mijinmu. Ka ɗauke mana kunyar da za mu sha.”
E sete mulheres n'aquelle dia lançarão mão d'um homem, dizendo: Nós comeremos do nosso pão, e nos vestiremos de nossos vestidos: tão sómente que sejamos chamadas pelo teu nome; tira o nosso opprobrio.
2 A wannan rana Reshen Ubangiji zai zama kyakkyawa da kuma ɗaukaka, kuma amfanin ƙasar zai zama abin fariya da ɗaukakar waɗanda suka rayu a Isra’ila.
N'aquelle dia o Renovo do Senhor será um ornamento e uma gloria; e o fructo da terra excellente e formoso para os que escaparem d'Israel.
3 Waɗanda suka rage a Sihiyona, waɗanda suka rage a Urushalima, za a ce da su masu tsarki, wato, dukan waɗanda aka rubuta a cikin masu rai a Urushalima.
E será que aquelle que ficar de resto em Sião, e o que ficar em Jerusalem, será chamado sancto: todo aquelle que em Jerusalem está escripto para vida;
4 Ubangiji zai wanke duk wani ƙazantar matan Sihiyona; ya tsabtacce jinin da aka zubar daga Urushalima ta wurin ruhun hukunci da yake ƙuna kamar wuta.
Quando o Senhor lavar a immundicia das filhas de Sião, e limpar o sangue de Jerusalem do meio d'ella, com o espirito de juizo, e com o espirito de ardor.
5 Sa’an nan Ubangiji zai sa girgijen hayaƙi da rana da harshen wuta da dare a bisa dukan Dutsen Sihiyona da kuma bisa waɗanda suka tattaru a can; a bisa duka kuwa ɗaukakar za tă zama rumfa.
E creará o Senhor sobre toda a habitação do monte de Sião, e sobre as suas congregações, uma nuvem de dia, e um fumo, e um resplandor de fogo chammejante de noite; porque sobre toda a gloria haverá protecção.
6 Za tă zama rumfa da inuwar da za tă tare zafin rana, da kuma mafaka da wurin ɓuya daga hadari da ruwan sama.
E haverá um tabernaculo para sombra com o calor do dia: e para refugio e esconderijo contra o alagamento e contra a chuva.

< Ishaya 4 >