< Ishaya 35 >

1 Hamada da ƙeƙasasshiyar ƙasa za su yi murna; jeji zai yi farin ciki ya kuma hudo. Kamar fure,
Çöl ve kurak toprak sevinecek, Bozkır coşup çiğdem gibi çiçeklenecek.
2 zai buɗu ya hudo; zai yi farin ciki mai girma ya kuma yi sowa don farin ciki. Za a maido wa Lebanon da darajarta, darajar Karmel da Sharon; za su ga ɗaukakar Ubangiji, darajar Allahnmu.
Her yanı çiçeklenip sevinçle coşacak, Sevincini haykıracak. Lübnan'ın yüceliği, Karmel ve Şaron'un görkemi ona verilecek. İnsanlar RAB'bin yüceliğini, Tanrımız'ın görkemini görecek.
3 Ku ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi, ku ƙarfafa gwiwoyin da suka gaji;
Gevşek elleri güçlendirin, Pekiştirin çözülen dizleri.
4 ku faɗa wa waɗanda suka karai a zukata, “Ku yi ƙarfin hali, kada ku ji tsoro; Allahnku zai zo, zai zo domin ya ɗau fansa; da ramuwar Allah zai zo don yă cece ku.”
Yüreği kaygılı olanlara, “Güçlü olun, korkmayın” deyin, “İşte Tanrınız geliyor! Öç almaya, karşılık vermeye geliyor. Sizi O kurtaracak.”
5 Sa’an nan idanun makafi za su buɗe kunnuwan kurame kuma su ji.
O zaman körlerin gözleri, Sağırların kulakları açılacak;
6 Sa’an nan guragu za su yi tsalle kamar barewa, bebaye kuma su yi sowa don farin ciki. Ruwa zai kwararo daga jeji rafuffuka kuma a cikin hamada.
Topallar geyik gibi sıçrayacak, Sevinçle haykıracak dilsizlerin dili. Çünkü çölde sular fışkıracak, Irmaklar akacak bozkırda.
7 Yashi mai ƙuna zai zama tafki, ƙeƙasasshiyar ƙasa kuma za tă cika da maɓulɓulan rafuffuka. A mazaunin diloli, inda suka taɓa zama, ciyawa da iwa da kyauro za su yi girma.
Kızgın kum havuza, Susuz toprak pınara dönüşecek. Çakalların yattığı yerlerde Kamış, saz ve ot bitecek.
8 Kuma babbar hanya za tă kasance a can; za a ce ta ita Hanyar Mai Tsarki. Marasa tsarki ba za su yi tafiya a kanta ba; za tă zama domin waɗanda suka yi tafiya a wannan Hanya ce; mugaye da wawaye ba za su yi ta yawo a kanta ba.
Orada bir yol, bir anayol olacak, “Kutsal yol” diye anılacak, Murdar kişiler geçemeyecek oradan. O yol kurtulmuş olanların yoludur. O yolda yürüyenler, bön kişiler de olsa yoldan sapmayacak.
9 Zaki ba zai kasance a can ba, balle wani naman jeji mai faɗa ya haura kanta; ba za a same su a can ba. Amma fansassu ne kaɗai za su yi tafiya a can,
Aslan olmayacak orada, Yırtıcı hayvan o yola çıkmayacak; Orada bulunmayacaklar. Ancak kurtulmuş olanlar yürüyecek o yolda.
10 kuma fansassu na Ubangiji za su komo. Za su shiga Sihiyona da rerawa; matuƙar farin ciki zai mamaye su. Murna da farin ciki za su sha kansu, baƙin ciki kuma da nishi za su gudu.
RAB'bin kurtardıkları dönecek, Sevinçle haykırarak Siyon'a varacaklar. Yüzlerinde sonsuz sevinç olacak. Onların olacak coşku ve sevinç, Üzüntü ve inilti kaçacak.

< Ishaya 35 >