< Ishaya 35 >

1 Hamada da ƙeƙasasshiyar ƙasa za su yi murna; jeji zai yi farin ciki ya kuma hudo. Kamar fure,
Inkangala lelizwe elomileyo kuzathokoza; inkangala izajabula iqhakaze. Njengeluba
2 zai buɗu ya hudo; zai yi farin ciki mai girma ya kuma yi sowa don farin ciki. Za a maido wa Lebanon da darajarta, darajar Karmel da Sharon; za su ga ɗaukakar Ubangiji, darajar Allahnmu.
izakhahlela, ithokoze kakhulu, ihlabele isithi. Inkazimulo yaseLebhanoni izanikezwa kuyo ubuhle beKhameli leSharoni, kuzabona inkazimulo kaThixo lobukhosi bukaNkulunkulu wethu.
3 Ku ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi, ku ƙarfafa gwiwoyin da suka gaji;
Qinisani izandla ezibuthakathaka, liqinise lamadolo axegayo;
4 ku faɗa wa waɗanda suka karai a zukata, “Ku yi ƙarfin hali, kada ku ji tsoro; Allahnku zai zo, zai zo domin ya ɗau fansa; da ramuwar Allah zai zo don yă cece ku.”
tshonini kulabo abalezinhliziyo ezilokwesaba lithi: “Qinani, lingesabi; uNkulunkulu wenu uzakuza, uzakuza ezophindisela, ajezise ngokulunga uzakuza ukuba alikhulule.”
5 Sa’an nan idanun makafi za su buɗe kunnuwan kurame kuma su ji.
Lapho-ke amehlo eziphofu azavuleka, lezindlebe zezacuthe zivuleke.
6 Sa’an nan guragu za su yi tsalle kamar barewa, bebaye kuma su yi sowa don farin ciki. Ruwa zai kwararo daga jeji rafuffuka kuma a cikin hamada.
Lapho-ke abaqhulayo bazakweqa njengempala, izimungulu zihlabele ngokuthokoza. Amanzi azampompoza ogwaduleni, izifula zigeleze enkangala.
7 Yashi mai ƙuna zai zama tafki, ƙeƙasasshiyar ƙasa kuma za tă cika da maɓulɓulan rafuffuka. A mazaunin diloli, inda suka taɓa zama, ciyawa da iwa da kyauro za su yi girma.
Itshebetshebe elitshisayo lizakuba yisiziba, umhlabathi owomileyo ube yimithombo echaphaka amanzi. Ezindaweni amakhanka ake ahlala kuzo, utshani lemihlanga lebhuma kuzakhula khona.
8 Kuma babbar hanya za tă kasance a can; za a ce ta ita Hanyar Mai Tsarki. Marasa tsarki ba za su yi tafiya a kanta ba; za tă zama domin waɗanda suka yi tafiya a wannan Hanya ce; mugaye da wawaye ba za su yi ta yawo a kanta ba.
Njalo kuzakuba lomgwaqo omkhulu: uzathiwa yiNdlela yobuNgcwele, izakuba ngeyalabo abahamba ngokuqonda. Abangcolileyo kabayikuhamba kuwo; uzakuba ngowalabo abahamba kuleyoNdlela lezithutha ezonayo kaziyikuhambahamba kuwo.
9 Zaki ba zai kasance a can ba, balle wani naman jeji mai faɗa ya haura kanta; ba za a same su a can ba. Amma fansassu ne kaɗai za su yi tafiya a can,
Akuyikuba lesilwane khona, loba esinye isilo esilolaka; sivuke kuwo kaziyikutholwa khona. Kodwa abahlengiweyo yibo kuphela abazahamba lapho,
10 kuma fansassu na Ubangiji za su komo. Za su shiga Sihiyona da rerawa; matuƙar farin ciki zai mamaye su. Murna da farin ciki za su sha kansu, baƙin ciki kuma da nishi za su gudu.
njalo labahlengiweyo bakaThixo bazabuyela. Bazangena eZiyoni behlabelela, intokozo engapheliyo izakuba ngumqhele emakhanda abo. Bazakuba lokuthula lenjabulo, usizi lokububula kuzaphela.

< Ishaya 35 >