< Ishaya 31 >

1 Kaiton waɗanda suka gangara zuwa Masar don neman taimako, waɗanda suke dogara ga dawakai, waɗanda suke dogara ga yawan kekunan yaƙinsu da kuma a girman ƙarfin mahayan dawakansu, amma ba sa dogara ga Mai Tsarkin nan na Isra’ila, ko ya nemi taimako daga Ubangiji.
Woe to those who go down to Egypt for help, and rely on horses, and trust in chariots because they are many, and in horsemen because they are very strong, but they look not to the Holy One of Israel, nor seek Jehovah!
2 Shi ma yana da hikima kuma zai iya kawo masifa; ba ya janye kalmominsa. Zai yi gāba da gidan mugu, gāba da waɗanda suke taimakon masu aikata mugunta.
Yet he also is wise, and will bring evil, and will not call back his words, but will arise against the house of the evildoers, and against the help of those who work iniquity.
3 Amma Masarawa mutane ne ba Allah ba; dawakansu nama da jini ne ba ruhu ba. Sa’ad da Ubangiji ya miƙa hannunsa, shi da yake taimako zai yi tuntuɓe shi da aka taimaka zai fāɗi; dukansu biyu za su hallaka tare.
Now the Egyptians are men, and not God, and their horses flesh, and not spirit. And when Jehovah shall stretch out his hand, both he who helps shall stumble, and he who is helped shall fall, and they shall all be consumed together.
4 Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Kamar yadda zaki kan yi ruri babban zaki a kan abin da ya yi farauta, kuma ko da yake dukan ƙungiyar makiyaya sun taru wuri ɗaya a kansa, ba zai jijjigu ta wurin ihunsu ba ko ya damu da kiraye-kirayensu, ta haka Ubangiji Maɗaukaki zai sauko don yă yi yaƙi a kan Dutsen Sihiyona da kuma a kan ƙwanƙolinsa.
For thus says Jehovah to me, As the lion and the young lion growling over his prey, even if a multitude of shepherds are called forth against him, he will not be dismayed at their voice, nor abase himself for the noise of them, so Jehovah of hosts will come down to fight upon mount Zion, and upon the hill of it.
5 Kamar tsuntsaye masu shawagi a sama haka Ubangiji Maɗaukaki zai kiyaye Urushalima; zai kāre ta ya kuma fanshe ta, zai ‘ƙetare’ ta ya kuma kuɓutar da ita.”
As birds hovering, so Jehovah of hosts will protect Jerusalem. He will protect and deliver. He will pass over and preserve.
6 Ku dawo gare shi ku da kuka yi masa babban tayarwa, ya Isra’ilawa.
Turn ye to him from whom ye have deeply revolted, O sons of Israel.
7 Gama a wannan rana kowannenku zai ƙi gumakan azurfa da zinariya da hannuwanku masu zunubi suka yi.
For in that day they shall cast away every man his idols of silver, and his idols of gold, which your own hands have made to you for a sin.
8 “Za a karkashe Assuriyawa da takobin da ba na yin mutum ba; takobi, da ba na yin mutum ba, zai cinye. Za su gudu daga takobi za a kuma sa samarinsu aikin dole.
And the Assyrian shall fall by the sword, not of man, and the sword, not of men, shall devour him. But he shall flee from the sword, and his young men shall become subject to task work.
9 Kagararsu za tă fāɗi saboda razana; da ganin matsayin yaƙin, shugabannin yaƙinsu za su firgita,” in ji Ubangiji, wanda wutarsa tana a Sihiyona, wanda matoyarsa tana a Urushalima.
And his rock shall pass away because of terror, and his rulers shall be dismayed at the ensign, says Jehovah, whose fire is in Zion, and his furnace in Jerusalem.

< Ishaya 31 >