< Ishaya 3 >

1 Yanzu ka duba fa, Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana shirin yă ɗauke kowane tanadi da taimako daga Urushalima da Yahuda dukan tanade-tanaden abinci da kuma dukan tanade-tanaden ruwa,
Porque, eis que o Senhor Deus dos Exercitos tirará de Jerusalem e de Judah o bordão e o cajado: a todo o sustento de pão, e a toda a borda d'agua;
2 jarumi, da soja, alƙali da annabi masu duba da dattijo,
Ao valente, e ao soldado, ao juiz, e ao propheta, e ao adivinho, e ao ancião,
3 shugaban sojojin hamsin da mutum mai makami, mai ba da shawara, gwanin sarrafa abubuwa da mai gwanintan dabo.
Ao capitão de cincoenta, e ao respeitavel, e ao conselheiro, e ao sabio entre os artifices, e ao eloquente.
4 “Zan sa’yan yara su zama shugabanninsu;’yan yara kurum za su yi mulkinsu.”
E dar-lhes-hei mancebos por principes, e creanças dominarão sobre elles.
5 Mutane za su zalunci juna mutum da mutum, maƙwabci da maƙwabci. Yara za su rena tsofaffi, ƙasƙantacce zai rena mai daraja.
E o povo será opprimido; um será contra o outro, e cada um contra o seu proximo: o menino se atreverá contra o ancião, e o vil contra o nobre.
6 Mutum zai kama ɗaya daga cikin’yan’uwansa a gidan mahaifinsa ya ce, “Kana da abin sawa, ka zama shugabanmu; wannan kango kuma yă zama a ƙarƙashinka!”
Quando algum travar de seu irmão da casa de seu pae, dizendo: Capa tens, sê nosso principe, e toma sob a tua mão esta ruina;
7 Amma a ranan nan zai tā da murya ya ce, “Ba ni ba dai. Ba ni da abinci ko abin sawa a gidana; kada ka mai da ni shugaban mutane.”
Então levantará a sua voz n'aquelle dia, dizendo: Não posso ser medico, nem tão pouco ha em minha casa pão, nem vestido algum: não me ponhaes por principe do povo.
8 Urushalima tana tangaɗi, Yahuda yana fāɗuwa; maganganunsu da ayyukansu suna gāba da Ubangiji, suna rena ɗaukakar kasancewarsa.
Porque tropeçou Jerusalem, e Judah é caido; porquanto a sua lingua e as suas obras são contra o Senhor, para irritarem os olhos da sua gloria.
9 Fuskokinsu shaidu ne a kansu; suna nuna zunubinsu a fili kamar yadda Sodom ya yi; ba sa ma ɓoye shi. Kaitonsu! Sun jawo wa kansu masifa.
A apparencia das suas faces testifica contra elles; e publicam os seus peccados como Sodoma; não os dissimulam: ai da sua alma! porque se fazem mal a si mesmos.
10 Ku faɗa wa masu adalci cewa kome zai zama musu da kyau, gama za su ji daɗin aikin da hannuwansu suka yi.
Dizem ao justo que bem lhe irá; que comerão do fructo das suas obras.
11 Kaiton masu mugunta! Masifa tana a kansu! Za a rama abin da hannuwansu suka yi.
Ai do impio! mal lhe irá: porque o galardão das suas mãos se lhe dará.
12 Matasa suna zalunta mutanena, mata suna mulki a bisansu. Ya mutanena, jagorarinku suna ɓad da ku; suna karkatar da ku daga hanya.
Os exactores do meu povo são creanças, e mulheres dominam sobre elle: ah, povo meu! os que te guiam te enganam, e devoram o caminho das tuas veredas.
13 Ubangiji ya ɗauki mazauninsa a cikin ɗakin shari’a; ya tashi don yă shari’anta mutane.
O Senhor se apresenta a pleitear, e se põe a julgar os povos.
14 Ubangiji yana shari’a da dattawa da kuma shugabannin mutanensa, “Ku ne kuka lalace gonar inabina; ganimar talakawa suna a gidajenku.
O Senhor vem em juizo contra os anciãos do seu povo, e contra os seus principes; porque vós consumistes esta vinha, o despojo do afflicto está em vossas casas.
15 Ina dalilin da kuke marmatsa mutanena kuna gurgurje fuskokin talakawa?” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
Que tendes vós, que atropellaes o meu povo e moeis as faces dos afflictos? diz o Senhor, o Deus dos Exercitos.
16 Ubangiji ya ce, “Matan Sihiyona suna da girman kai, suna tafiya da wuya a miƙe, da idanu masu yaudara, suna takawa ɗaya-ɗaya a hankali, da mundaye a ƙafafunsu, suna cas-cas.
Diz ainda mais o Senhor: Porquanto as filhas de Sião se exalçam, e andam com o pescoço emproado, fazendo acenos com os olhos, e, indo andando, andam como dançando, e cascavelando com os pés
17 Saboda haka Ubangiji zai kawo gyambuna a kawunan matan Sihiyona; Ubangiji zai sa a aske kawunansu, a bar su ƙwal.”
Portanto o Senhor fará calva a mioleira das filhas de Sião, e o Senhor descobrirá as suas vergonhas.
18 A wannan rana Ubangiji zai ƙwace abin da suke taƙama da shi, mundayensu, ɗankwalin kansu da abin wuyansu,
N'aquelle dia tirará o Senhor o enfeite das ligas, e as redezinhas, e as luetas,
19 ’yan kunnensu, kwandagansu da lulluɓinsu,
Os pendentes, e as manilhas, e os vestidos resplandecentes,
20 kitsonsu, sarƙar da suke sa wa damatsansu da ɗamararsu, kwalabai turare da layu,
Os diademas, e os enfeites dos braços, e os cendaes, e as bocetas cheirosas, e as arrecadas,
21 da ƙawanen da suka sa a yatsotsinsu da hancinsu,
Os anneis, e as joias pendentes do nariz,
22 tufafi masu kyau, da manyan rigunansu, da mayafansu, da jakar kuɗinsu
Os vestidos de festa, e os mantos, e as coifas, e os alfinetes,
23 da madubi, da kuma tufafin lilin da adikai, da gyale.
Os espelhos, e as capinhas de linho finissimas, e as toucas, e os véus.
24 A maimakon ƙanshi, wari ne za a ji; a maimakon abin ɗamara, igiya ce za a samu; a maimakon kyakkyawan gashi, sanƙo za su kasance da shi a kai; a maimakon tufafi masu kyau, za su sa tsummoki; a maimakon kyau, za su zama munana.
E será que em logar de cheiro suave haverá fedor; e por cinto uma corda; e em logar d'encrespadura de cabellos, calva; e em logar de veste larga, cingimento de sacco; e queimadura em logar de formosura.
25 Mazanku za su mutu ta wurin takobi, jarumawanku za su mutu a yaƙi.
Teus varões cairão á espada, e teus valentes na peleja.
26 Ƙofofin Sihiyona za su yi makoki su kuma yi kuka; za tă zama wofi, za tă zauna a ƙasa.
E as suas portas gemerão e prantearão; e ella, ficando desolada, se assentará no chão.

< Ishaya 3 >