< Ishaya 27 >

1 A wannan rana, Ubangiji zai yi hukunci da takobi, takobinsa mai tsanani, mai ƙarfi da kuma mai muguwar ɓarna, zai hukunta dodon ruwa macijin nan da ya kanannaɗe, dodon ruwa macijin nan mai murɗewa; zai kashe dodon nan na teku.
En ce jour, l’Eternel châtiera de sa forte, grande et puissante épée le léviathan, serpent droit comme une barre, et le léviathan, serpent aux replis tortueux; il fera périr aussi le monstre qui habite la mer.
2 A wannan rana, “Ku rera game da gonar inabi mai ba da’ya’ya ku ce
En ce jour, entonnez à son intention le chant de la Vigne de délices:
3 Ni, Ubangiji na lura da ita; na yi ta yin mata banruwa. Na yi tsaronta dare da rana don kada wani yă yi mata ɓarna.
Moi, l’Eternel, je suis son gardien, à toute heure je l’arrose. Pour que nul ne la maltraite, nuit et jour je la surveille.
4 Ban yi fushi ba. Da a ce ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suke kalubalanta na mana! Zan fita in yi yaƙi da su; da na sa musu wuta duka.
De ressentiment, il n’y en a point chez moi; dussé-je en avoir, contre les ronces et les épines je marcherais en combattant, et d’un coup y mettrais le feu.
5 Ko kuma bari su zo wurina don mafaka; bari su yi sulhu da ni, I, bari su yi sulhu da ni.”
Mais plutôt qu’on s’attache à ma protection, qu’on fasse la paix avec moi, qu’avec moi on fasse la paix!
6 A kwanaki masu zuwa Yaƙub zai yi saiwa, Isra’ila zai yi toho ya kuma yi fure ya cika dukan duniya da’ya’ya.
Aux temps futurs, Jacob étendra ses racines, Israël donnera des bourgeons et des fleurs, et ils couvriront de fruits la surface du globe.
7 Ubangiji ya buge shi kamar yadda ya bugi waɗanda suka buge shi? An kashe shi kamar yadda aka kashe waɗanda suka kashe shi?
Dieu les a-t-il frappés comme il frappa leurs agresseurs? Ont-ils péri comme périrent les victimes atteintes par lui?
8 Ta wurin yaƙi da zaman bauta ka hukunta shi, da tsananin tsawa kuma ka kore shi, kamar a ranar da iskar gabas ta hura.
C’Est avec modération que tu as puni ce peuple en le congédiant, alors qu’au jour de la tempête tu as fait souffler un vent puissant.
9 A ta haka fa, za a yi kafarar laifin Yaƙub, wannan kuma zai zama cikakken amfanin kau da zunubinsa. Sa’ad da ya niƙa duwatsun bagade suka zama kamar allin da aka farfashe kucu-kucu, har ba sauran ginshiƙan Ashera ko bagadan ƙona turare da za a bari a tsaye.
Or, voici comment sera effacée l’iniquité de Jacob et à quel prix disparaîtra sa faute: qu’il réduise en poussière toutes les pierres des autels comme de vils plâtras, que statues d’Astarté, statues du soleil tombent sans retour!
10 Birni mai katanga ya zama kufai, yasasshen mazauni, an yashe shi kamar hamada; a can’yan maruƙa suke kiwo, a can suke kwance; sun kakkaɓe rassanta ƙaf.
Mais cette ville si forte sera une solitude, cette résidence sera vide et abandonnée comme une plaine sauvage: la génisse y viendra paître, elle s’y couchera, elle en broutera les jeunes pousses.
11 Sa’ad da rassanta suka bushe, sai su kakkarye su mata kuma su zo su yi itacen wuta da su. Gama mutane ne marar azanci; saboda haka Mahaliccinsu bai ji tausayinsu ba, Mahaliccinsu bai nuna musu jinƙai ba.
Le branchage, une fois devenu sec, sera brisé, et des femmes viendront y mettre le feu parce que c’est un peuple inintelligent; aussi son Auteur sera pour lui sans clémence, et son Créateur ne lui fera point grâce.
12 A wannan rana Ubangiji zai tankaɗe daga Yuferites mai gudu zuwa Rafin Masar, ku kuma, ya Isra’ilawa, za a tattara ku ɗaya-ɗaya.
Il arrivera en ce jour que l’Eternel fera un abatis de fruits, depuis les flots de l’Euphrate jusqu’au torrent d’Egypte; mais vous, enfants d’Israël, vous serez recueillis un à un.
13 Kuma a wannan rana zai busa ƙaho mai kāra sosai. Waɗanda suke mutuwa a Assuriya da kuma waɗanda aka kai zaman bauta a Masar za su zo su kuma yi wa Ubangiji sujada a dutse mai tsarki a Urushalima.
En ce jour résonnera la grande trompette; alors arriveront ceux qui étaient perdus dans le pays d’Achour, relégués dans la terre d’Egypte, et ils se prosterneront devant l’Eternel, sur la montagne sainte, à Jérusalem.

< Ishaya 27 >