< Ishaya 26 >

1 A wannan rana za a rera wannan waƙa a ƙasar Yahuda. Muna da birni mai ƙarfi; Allah yake ceton katanga da kuma kagarunta.
In that day this song is sung in the land of Judah: “We have a strong city, He makes salvation [for] walls and bulwark.
2 A buɗe ƙofofi saboda al’umma mai adalci ta shiga, al’ummar da mai aminci.
Open the gates, That a righteous nation may enter, Preserving steadfastness.
3 Za ka kiyaye shi da cikakken salama shi wanda ya kafa zuciyarsa gare ka, domin ya dogara a gare ka.
You keep [him] in peace [whose] imagination [is] stayed—peace! For he is confident in You.
4 Ku dogara ga Ubangiji, gama shi Ubangiji, ne madawwamin Dutse.
Trust in YHWH forever, For in YAH—YHWH [is] a rock of ages,
5 Yakan ƙasƙantar da waɗanda suke zama a bisa ya kawar da birni mai alfarma ƙasa; ya rusa ta har ƙasa ya jefar da ita cikin ƙura.
For He bowed down the dwellers on high, A city set on high He makes low, He makes it low to the earth, He causes it to come to the dust,
6 Ƙafafu sukan tattake ta, ƙafafu waɗanda aka zalunta, wato, sawun matalauta.
A foot treads it down, Feet of the poor—steps of the weak.
7 Hanyar masu adalci sumul take; Ya Mai Aikata Gaskiya, ka sa hanyar masu adalci ta yi sumul.
The path for the righteous [is] uprightness, O upright One, You ponder the path of the righteous.
8 I, Ubangiji, cikin tafiya a hanyar dokokinka, muna sa zuciya gare ka; sunanka da tunani a kanka su ne marmarin zukatanmu.
Also, [in] the path of Your judgments, O YHWH, we have waited [for] You, To Your Name and to Your remembrance [Is] the desire of the soul.
9 Raina yana marmarinka da dare; da safe kuma raina yana son ganinka. Sa’ad da hukunce-hukuncenka suka sauko duniya, mutanen duniya kan koyi adalci.
I desired You in the night [with] my soul, Also, I seek You earnestly [with] my spirit within me, For when Your judgments [are] on the earth, The inhabitants of the world have learned righteousness.
10 Ko da yake akan nuna wa mugaye alheri, ba sa koyi adalci; har ma a ƙasar masu aikata gaskiya sukan ci gaba da aikata mugunta ba sa ganin girmar darajar Ubangiji.
The wicked finds favor, He has not learned righteousness, He deals perversely in a land of straightforwardness, And does not see the excellence of YHWH.
11 Ya Ubangiji an ɗaga hannunka sama, amma ba sa ganinsa. Bari su ga himmarka don mutanenka su kuma sha kunya; bari wutar da aka ajiye don abokan gābanka ta cinye su.
O YHWH, Your hand [is] high—they do not see, They see the zeal of the people, and are ashamed, Also, the fire consumes Your adversaries.
12 Ubangiji ka kafa salama dominmu; duk abin da muka iya yi kai ne ka yi mana.
O YHWH, You appoint peace to us, For You have also worked all our works for us.
13 Ya Ubangiji, Allahnmu, waɗansu iyayengiji ban da kai sun yi mulki a kanmu, amma sunanka kaɗai muka girmama.
O our God YHWH, lords have ruled us besides You, Only, by You we make mention of Your Name.
14 Yanzu duk sun mutu, ba za su ƙara rayuwa ba; waɗannan ruhohin da suka rasu ba za su tashi ba. Ka hukunta su ka kuma kawo su ga hallaka; ka sa ba za a ƙara tunawa da su ba.
Dead—they do not live, Rephaim, they do not rise, Therefore You have inspected and destroy them, Indeed, you destroy all their memory.
15 Ka fadada al’umma, ya Ubangiji; ka fadada al’umma. Ka samo wa kanka ɗaukaka; ka fadada dukan iyakokin ƙasar.
You have added to the nation, O YHWH, You have added to the nation, You have been honored, You have put all the ends of the earth far off.
16 Ubangiji, sun zo gare ka a cikin damuwarsu; sa’ad da ka hore su, da ƙyar suna iya yin addu’a.
O YHWH, in distress they missed You, They have poured out a whisper, Your discipline [is] on them.
17 Kamar mace mai ciki da take gab da haihuwa takan yi ta murɗawa tana kuka saboda zafi, haka muka kasance a gabanka, ya Ubangiji.
When a pregnant woman comes near to the birth, She is pained—she cries in her pangs, So we have been from Your face, O YHWH.
18 Muna da ciki, mun yi ta murɗewa saboda zafi, amma mun haifi iska. Ba mu kawo ceto ga duniya ba; ba mu haifi mutanen duniya ba.
We have conceived, we have been pained. We have brought forth, as it were, wind, We do not work salvation in the earth, Nor do the inhabitants of the world fall.
19 Amma matattunka za su rayu; jikunansu za su tashi. Ku da kuke zama a ƙura, ku farka ku kuma yi sowa don farin ciki. Raɓarka kamar raɓar safiya ce; duniya za tă haifi matattunta.
Your dead live—My dead body, they rise. Awake and sing, you dwellers in the dust, For the dew of herbs [is] your dew, And you cause the land of Rephaim to fall.
20 Ku tafi, mutanena, ku shiga ɗakunanku ku kuma kulle ƙofofi; ku ɓoye kanku na ɗan lokaci sai ya huce fushinsa.
Come, My people, enter into your inner chambers, And shut your doors behind you, Hide yourself shortly [for] a moment until the indignation passes over.
21 Duba, Ubangiji yana fitowa daga mazauninsa don yă hukunta mutanen duniya saboda zunubansu. Duniya za tă bayyana zub da jinin da aka yi a kanta; ba za tă ƙara ɓoye waɗanda aka kashe a cikinta ba.
For behold, YHWH is coming out of His place, To charge the iniquity of the inhabitant of the earth on him, And the earth has revealed her blood, Nor does she cover her slain anymore!”

< Ishaya 26 >