< Ishaya 26 >

1 A wannan rana za a rera wannan waƙa a ƙasar Yahuda. Muna da birni mai ƙarfi; Allah yake ceton katanga da kuma kagarunta.
In that day shall this song be sung in the land of Iudah, We haue a strong citie: saluation shall God set for walles and bulwarkes.
2 A buɗe ƙofofi saboda al’umma mai adalci ta shiga, al’ummar da mai aminci.
Open ye the gates that the righteous nation, which keepeth the trueth, may enter in.
3 Za ka kiyaye shi da cikakken salama shi wanda ya kafa zuciyarsa gare ka, domin ya dogara a gare ka.
By an assured purpose wilt thou preserue perfite peace, because they trusted in thee.
4 Ku dogara ga Ubangiji, gama shi Ubangiji, ne madawwamin Dutse.
Trust in the Lord for euer: for in the Lord God is strength for euermore.
5 Yakan ƙasƙantar da waɗanda suke zama a bisa ya kawar da birni mai alfarma ƙasa; ya rusa ta har ƙasa ya jefar da ita cikin ƙura.
For hee will bring downe them that dwell on hie: the hie citie he will abase: euen vnto the ground wil he cast it downe, and bring it vnto dust.
6 Ƙafafu sukan tattake ta, ƙafafu waɗanda aka zalunta, wato, sawun matalauta.
The foote shall treade it downe, euen the feete of the poore, and the steppes of the needie.
7 Hanyar masu adalci sumul take; Ya Mai Aikata Gaskiya, ka sa hanyar masu adalci ta yi sumul.
The way of the iust is righteousnesse: thou wilt make equall the righteous path of the iust.
8 I, Ubangiji, cikin tafiya a hanyar dokokinka, muna sa zuciya gare ka; sunanka da tunani a kanka su ne marmarin zukatanmu.
Also we, O Lord, haue waited for thee in the way of thy iudgemets: the desire of our soule is to thy Name, and to the remembrance of thee.
9 Raina yana marmarinka da dare; da safe kuma raina yana son ganinka. Sa’ad da hukunce-hukuncenka suka sauko duniya, mutanen duniya kan koyi adalci.
With my soule haue I desired thee in the night, and with my spirit within mee will I seeke thee in the morning: for seeing thy iudgements are in the earth, the inhabitants of the world shall learne righteousnesse.
10 Ko da yake akan nuna wa mugaye alheri, ba sa koyi adalci; har ma a ƙasar masu aikata gaskiya sukan ci gaba da aikata mugunta ba sa ganin girmar darajar Ubangiji.
Let mercie bee shewed to the wicked, yet hee will not learne righteousnesse: in the land of vprightnesse will he do wickedly, and will not beholde the maiestie of the Lord.
11 Ya Ubangiji an ɗaga hannunka sama, amma ba sa ganinsa. Bari su ga himmarka don mutanenka su kuma sha kunya; bari wutar da aka ajiye don abokan gābanka ta cinye su.
O Lord, they will not beholde thine hie hande: but they shall see it, and bee confounded with the zeale of the people, and the fire of thine enemies shall deuoure them.
12 Ubangiji ka kafa salama dominmu; duk abin da muka iya yi kai ne ka yi mana.
Lord, vnto vs thou wilt ordeine peace: for thou also hast wrought all our workes for vs.
13 Ya Ubangiji, Allahnmu, waɗansu iyayengiji ban da kai sun yi mulki a kanmu, amma sunanka kaɗai muka girmama.
O Lord our God, other lords beside thee, haue ruled vs, but we will remember thee onely, and thy Name.
14 Yanzu duk sun mutu, ba za su ƙara rayuwa ba; waɗannan ruhohin da suka rasu ba za su tashi ba. Ka hukunta su ka kuma kawo su ga hallaka; ka sa ba za a ƙara tunawa da su ba.
The dead shall not liue, neither shall the dead arise, because thou hast visited and scattered them, and destroyed all their memorie.
15 Ka fadada al’umma, ya Ubangiji; ka fadada al’umma. Ka samo wa kanka ɗaukaka; ka fadada dukan iyakokin ƙasar.
Thou hast increased the nation, O Lord: thou hast increased the nation: thou art made glorious: thou hast enlarged all the coastes of the earth.
16 Ubangiji, sun zo gare ka a cikin damuwarsu; sa’ad da ka hore su, da ƙyar suna iya yin addu’a.
Lord, in trouble haue they visited thee: they powred out a prayer when thy chastening was vpon them.
17 Kamar mace mai ciki da take gab da haihuwa takan yi ta murɗawa tana kuka saboda zafi, haka muka kasance a gabanka, ya Ubangiji.
Like as a woman with childe, that draweth neere to the trauaile, is in sorow, and cryeth in her paines, so haue we bene in thy sight, O Lord.
18 Muna da ciki, mun yi ta murɗewa saboda zafi, amma mun haifi iska. Ba mu kawo ceto ga duniya ba; ba mu haifi mutanen duniya ba.
We haue coceiued, we haue borne in paine, as though we should haue brought forth winde: there was no helpe in the earth, neither did the inhabitants of the world fall.
19 Amma matattunka za su rayu; jikunansu za su tashi. Ku da kuke zama a ƙura, ku farka ku kuma yi sowa don farin ciki. Raɓarka kamar raɓar safiya ce; duniya za tă haifi matattunta.
Thy dead men shall liue: euen with my body shall they rise. Awake, and sing, ye that dwel in dust: for thy dewe is as the dew of herbes, and the earth shall cast out the dead.
20 Ku tafi, mutanena, ku shiga ɗakunanku ku kuma kulle ƙofofi; ku ɓoye kanku na ɗan lokaci sai ya huce fushinsa.
Come, my people: enter thou into thy chambers, and shut thy doores after thee: hide thy selfe for a very litle while, vntill the indignation passe ouer.
21 Duba, Ubangiji yana fitowa daga mazauninsa don yă hukunta mutanen duniya saboda zunubansu. Duniya za tă bayyana zub da jinin da aka yi a kanta; ba za tă ƙara ɓoye waɗanda aka kashe a cikinta ba.
For lo, the Lord commeth out of his place, to visite the iniquitie of the inhabitants of the earth vpon them: and the earth shall disclose her blood, and shall no more hide her slaine.

< Ishaya 26 >