< Ishaya 24 >

1 Duba, Ubangiji zai wofinta duniya ya kuma yi kaca-kaca da ita; zai ɓata fuskarta ya watsar da mazaunanta,
Voilà que le Seigneur va dévaster la terre; il va la rendre déserte; il va dévoiler sa face et disperser ceux qui habitent en elle.
2 zai zama abu ɗaya ga firist kamar yadda yake ga mutane, ga maigida kamar yadda yake ga bawa, ga uwargijiya kamar yadda yake ga baiwa, ga mai sayarwa kamar yadda yake ga mai saya, ga mai karɓan rance kamar yadda yake ga mai ba da rance, ga mai karɓan bashi kamar yadda yake ga mai ba da bashi.
Et le peuple sera comme le prêtre, le serviteur comme le maître, et la servante comme la maîtresse; le marchand sera comme l'acheteur, le préteur comme l'emprunteur, et le débiteur comme le créancier.
3 Za a wofinta duniya ƙaƙaf a kuma washe ta sarai. Ubangiji ne ya faɗa haka.
La terre sera entièrement détruite, la terre sera entièrement dépouillée; car la bouche du Seigneur a dit ces choses:
4 Duniya ta bushe ta kuma yanƙwane, duniya tana shan azaba ta kuma raunana, masu daraja na duniya suna shan azaba.
La terre est dans le deuil, le monde est désolé, les grands de la terre ont pleuré.
5 Duniya ta ƙazantu ta wurin mutanenta sun ƙi yin biyayya da dokoki, sun keta farillai suka kuma karya madawwamin alkawari.
Elle a péché par ceux qui l'habitent, parce qu'ils ont transgressé la loi et altéré les commandements de l'éternelle alliance.
6 Saboda haka la’ana za tă auko wa duniya; dole mutanenta su ɗauki hakkin laifinsu. Saboda haka aka ƙone mazaunan duniya, kuma kaɗan ne kurum suka rage.
C'est pourquoi une malédiction consumera cette terre en punition du péché de ceux qui l'habitent. C'est pourquoi ses habitants seront pauvres, et il n'y restera qu'un petit nombre d'hommes.
7 Sabon ruwan inabi ya bushe kuringar inabi kuma sun yanƙwane; dukan masu farin ciki suna nishi.
Le vin pleurera, la vigne pleurera; et ils gémiront, tous ceux qui avaient l'âme en joie;
8 Kaɗe-kaɗen garayu sun yi shiru, surutun masu murna ya daina, garayan farin ciki ya yi shiru.
Il a cessé, le bruit joyeux des tambours; elle a cessé, la voix de la cithare.
9 Babu sauran shan ruwan inabi suna rera waƙa; barasa ya zama da ɗaci ga masu shanta.
Les hommes sont confondus; ils ne boivent plus de vin, et la bière est pleine d'amertume pour ceux qui en boivent.
10 Birnin da aka birkice ta zama kango; an kulle ƙofar shiga kowane gida.
Toute la ville est déserte; elle ferme ses maisons pour qu'on n'y puisse entrer.
11 A tituna suna kukan neman ruwan inabi; dukan farin ciki ya dawo baƙin ciki, an hana dukan kaɗe-kaɗe a duniya.
Partout elle crie pour avoir du vin; toute joie sur la terre a cessé, toute joie est partie de la terre,
12 An bar birnin kango, aka yi kaca-kaca da ƙofofinta.
Et les villes seront inhabitées, et les maisons vides crouleront.
13 Haka zai zama a duniya da kuma a cikin al’ummai, kamar sa’ad da akan karkaɗe itacen zaitun, ko kuma kamar sa’ad da ake barin kala bayan an girbe inabi.
Toutes ces choses arriveront sur la terre au milieu des nations. Et de même que l'on secoue un olivier, ainsi seront-elles secouées. Et si la vendange s'arrête,
14 Sun daga muryoyinsu, sun yi sowa ta farin ciki; daga yamma sun furta darajar Ubangiji.
Ils pousseront de grandes clameurs; mais ceux qui auront été épargnés sur la terre se réjouiront tous ensemble de la gloire du Seigneur, et la mer en sera troublée dans ses eaux.
15 Saboda haka a gabas sun ɗaukaka Ubangiji, a ɗaukaka sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, a cikin tsibiran teku.
C'est pourquoi la gloire du Seigneur ira jusqu'aux îles de la mer, le nom du Seigneur y sera glorifié.
16 Daga iyakokin duniya mun ji waƙoƙi, “Ɗaukaka ga Mai Adalcin nan.” Amma na ce, “Na lalace, na lalace! Kaitona! Munafukai sun ci amana! Da munafunci munafukai sun ci amana!”
Seigneur Dieu d'Israël, des extrémités de la terre nous avons appris vos prodiges, vous, espérance de l'homme pieux. Et l'on dira: Malheur aux prévaricateurs qui transgressent la loi!
17 Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen duniya.
La peur, l'abîme et les pièges sont pour vous qui habitez la terre.
18 Duk wanda ya yi ƙoƙarin tserewa daga ƙarar razana zai fāɗa cikin rami; wanda kuma ya tsere daga rami za a kama shi a tarko. An buɗe ƙofofin ambaliyar ruwan sama, harsashen ginin duniya suna rawa.
Et voici ce qui arrivera: celui qui fuira de peur tombera dans l'abîme; et celui qui sortira de l'abîme sera pris au piège; car les cataractes du ciel seront ouvertes, et les fondements de la terre en seront ébranlés.
19 An tsage duniya, duniya ta farfashe ta wage, an girgiza duniya ƙwarai.
La terre sera pleine de trouble, la terre sera pleine d'angoisse.
20 Duniya tana tangaɗi kamar mashayi, tana lilo kamar rumfa a cikin iska; laifin tayarwarta ya yi nauyi sosai har ta fāɗi ba kuwa za tă ƙara tashi ba.
Elle s'est détournée de sa voie comme un homme ivre et débauché; elle sera chancelante comme la cabane du gardien des vergers; et parce que l'iniquité a prévalu en elle, elle tombera et ne pourra se relever.
21 A wannan rana Ubangiji zai hukunta ikokin da suke cikin sama da kuma sarakunan da suke a duniya.
Et le Seigneur étendra sa main sur l'armée du ciel et sur les rois de la terre.
22 Za a tattara su tare kamar ɗaurarru a kurkuku; za a rufe su a kurkuku a kuma hukunta su bayan kwanaki masu yawa.
Et la grande Synagogue de la terre sera réunie et jetée en prison; et la forteresse sera fermée; et après plusieurs générations ils seront visités.
23 Sa’an nan wata zai ruɗe, rana ta ji kunya; gama Ubangiji Maɗaukaki zai yi mulki a kan Dutsen Sihiyona da kuma a cikin Urushalima, da kuma a gaban dattawanta, da ɗaukaka.
Et la brique sera liquéfiée, et le mur croulera; parce que le Seigneur règnera du haut de Sion et de Jérusalem, et en présence des anciens il sera glorifié.

< Ishaya 24 >