< Ishaya 21 >
1 Abin da Allah ya faɗa game da Hamada da take kusa da Teku. Kamar guguwa mai share cikin ƙasar kudu, mai hari ya zo daga hamada, daga ƙasar mai banrazana.
A declaration about the desert by the sea. Like stormwinds sweeping through the Negev it comes passing through from the wilderness, from a terrible land.
2 An nuna mini mugun wahayi, mai bashewa ya bashe, mai washewa ya washe. Elam, ki yi yaƙi! Mediya, ki yi kwanto! Zan kawo ƙarshen dukan nishe-nishen da ta jawo.
A distressing vision has been given to me: the treacherous man deals treacherously, and the destroyer destroys. Go up and attack, Elam; besiege, Media; I will stop all her groaning.
3 Game da wannan jikina yana ciwo, zafi ya kama ni, kamar na mace mai naƙuda; na razana game da abin da na ji, na yi mamakin abin da na gani.
Therefore my loins are filled with pain; pains like the pains of a woman in labor have taken hold of me; I am bowed down by what I heard; I am disturbed by what I saw.
4 Gabana tana ta fāɗuwa, tsoro ya sa ina rawan jiki; hasken da nake marmari ya zo da razana gare ni.
My heart pounds; I shake with fear. Twilight was my desire, but it brought me terror.
5 Sun shirya teburori, sun shimfiɗa dardumai, sun ci, sun sha! Tashi, ku hafsoshi, sa mai a garkuwoyi!
They prepare the table, they spread rugs and eat and drink; arise, princes, anoint your shields with oil.
6 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Tafi, ka sa mai tsaro ka kuma sa ya ba da rahoton abin da ya gani.
For this is what the Lord said to me, “Go, post a watchman; he must report what he sees.
7 Sa’ad da ya ga kekunan yaƙi tare da ƙungiyoyin dawakai, mahaya a kan jakuna, ko mahaya a kan raƙuma, to, fa ya zauna a faɗake, ya kintsa sosai.”
When he sees a chariot, a pair of horsemen, riders on donkeys, and riders on camels, then he must pay attention and be very alert.”
8 Mai tsaron kuma ya yi ihu, “Kowace rana, ranka yă daɗe, nakan tsaya a hasumiyar tsaro; kowane dare nakan tsaya a wurin aikina.
The watchman cries out, “Lord, on the watchtower I stand all day, every day, and at my post I stand all night long.”
9 Duba, ga wani mutum tafe a keken yaƙin tare da ƙungiyar dawakai. Ya kuma mayar da amsa, ‘Babilon ta fāɗi, ta fāɗi! Dukan siffofin allolinta kwance a ragargaje a ƙasa!’”
Here comes a chariot with a man and a pair of horsemen. He calls out, “Babylon has fallen, fallen, and all the carved figures of its gods are broken to the ground.”
10 Ya mutanena, an ragargaje ku a masussuka, na faɗa muku abin da na ji daga Ubangiji Maɗaukaki, daga Allah na Isra’ila.
My threshed and winnowed ones, children of my threshing floor! What I have heard from Yahweh of hosts, the God of Israel, I have declared to you.
11 Abin da Allah ya faɗa game da Duma, Wani ya kira ni daga Seyir, “Mai tsaro, me ya rage a daren? Mai tsaro, me ya rage a daren?”
A declaration about Dumah. One calls to me from Seir, “Watchman, what is left of the night? Watchman, what is left of the night?”
12 Mai tsaro ya amsa, “Safiya ta gabato, haka kuma dare. In za ka yi tambaya, to, yi tambaya; sai ka sāke zuwa, ka tambaya.”
The watchman said, “The morning comes and also the night. If you want to ask, then ask; and come back again.”
13 Abin da Allah ya faɗa game da Arabiya. Ku ayarin Dedanawa, ku da kuka sauka a jejin Arabiya,
A declaration about Arabia. In the wilderness of Arabia you spend the night, you caravans of Dedanites.
14 ku kawo ruwa don ƙishirwa; ku da kuke zama a Tema, ku kawo abinci don masu gudun hijira.
Bring water for the thirsty; inhabitants of the land of Tema, meet the fugitives with bread.
15 Sun gudu daga takobi, daga takobin da aka janye, daga bakan da aka tanƙware da kuma daga zafin yaƙi.
For they have fled from the sword, from the drawn sword, from the bent bow, and from the weight of war.
16 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Cikin shekara ɗaya, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, dukan sojojin Kedar za su zo ga ƙarshe.
For this is what the Lord said to me, “Within a year, as a laborer hired for a year would see it, all the glory of Kedar will end.
17 Waɗanda suka yi rai na maharba, jarumawan Kedar, za su zama kaɗan.” Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa.
Only a few of the archers, the warriors of Kedar will remain,” for Yahweh, the God of Israel, has spoken.