< Ishaya 19 >
1 Abin da Allah ya faɗa game da Masar, Duba, Ubangiji yana a kan girgije a sukwane yana kuwa zuwa Masar. Gumakan Masar sun firgita a gabansa, zukatan Masarawa sun karai.
论埃及的默示: 看哪,耶和华乘驾快云, 临到埃及。 埃及的偶像在他面前战兢; 埃及人的心在里面消化。
2 “Zan tā da hargitsi tsakanin mutumin Masar da mutumin Masar, ɗan’uwa zai yi gāba da ɗan’uwa maƙwabci ya yi gāba da maƙwabci, birni ya yi gāba da birni, mulki ya yi gāba da mulki.
我必激动埃及人攻击埃及人— 弟兄攻击弟兄, 邻舍攻击邻舍; 这城攻击那城, 这国攻击那国。
3 Masarawa za su karai, zan kuma sa shirye-shiryensu su zama banza; za su nemi shawarar gumaka da kuma ruhohin matattu, za su nemi shawarar mabiya da na masu duba.
埃及人的心神必在里面耗尽; 我必败坏他们的谋略。 他们必求问偶像和念咒的、 交鬼的、行巫术的。
4 Zan ba da Masarawa ga ikon azzalumi shugaba, mugun sarki kuma zai yi mulki a kansu,” in ji mai girma, Ubangiji Maɗaukaki.
我必将埃及人交在残忍主的手中; 强暴王必辖制他们。 这是主—万军之耶和华说的。
5 Ruwayen kogi za su ƙafe, bakin kogi zai shanye yă kuma bushe.
海中的水必绝尽, 河也消没干涸。
6 Wuriyoyi za su yi wari; rafuffukan Masar za su yi ta raguwa har su ƙafe. Iwa da jema za su bushe,
江河要变臭; 埃及的河水都必减少枯干。 苇子和芦荻都必衰残;
7 haka ma tsire-tsire kusa da Nilu, a bakin kogi. Kowane abin da aka shuka a gefen Nilu zai bushe, iska ta kwashe su ƙaf.
靠尼罗河旁的草田, 并沿尼罗河所种的田,都必枯干。 庄稼被风吹去,归于无有。
8 Masu kamun kifi za su yi nishi su kuma yi makoki, dukan waɗanda suke jefan ƙugiyoyi a Nilu; waɗanda suke jefan abin kamun kifi a ruwa abin kamun kifin za su zama marasa amfani.
打鱼的必哀哭。 在尼罗河一切钓鱼的必悲伤; 在水上撒网的必都衰弱。
9 Waɗanda suke aiki da kaɗin auduga za su karai, masu yin lilin mai kyau za su fid da zuciya.
用梳好的麻造物的 和织白布的都必羞愧;
10 Masu aikin tufafi ransu zai ɓace, kuma dukan masu samun albashi za su damu.
国柱必被打碎, 所有佣工的,心必愁烦。
11 Shugabannin Zowan ba kome ba ne, wawaye ke kawai; mashawarta masu hikima na Fir’auna suna ba da shawarwari marasa amfani. Yaya za ka ce wa Fir’auna, “Ni ɗaya ne cikin masu hikima, almajirin sarakuna na dā can”?
琐安的首领极其愚昧; 法老大有智慧的谋士, 所筹划的成为愚谋。 你们怎敢对法老说: 我是智慧人的子孙, 我是古王的后裔?
12 Ina masu hikima suke yanzu? Bari su nuna maka su kuma sanar da abin da Ubangiji Maɗaukaki ya shirya a kan Masar.
你的智慧人在哪里呢? 万军之耶和华向埃及所定的旨意, 他们可以知道,可以告诉你吧!
13 Shugabannin Zowan sun zama wawaye, an ruɗe shugabannin Memfis dutsen kan kusurwa na mutanenta su sa Masar ta kauce.
琐安的首领都变为愚昧; 挪弗的首领都受了迷惑。 当埃及支派房角石的, 使埃及人走错了路。
14 Ubangiji ya sa zuba musu ruhun jiri; suka sa Masar ta yi tangaɗi cikin kome da take yi, kamar yadda mutumin da ya bugu yake tangaɗi cikin amansa.
耶和华使乖谬的灵搀入埃及中间; 首领使埃及一切所做的都有差错, 好像醉酒之人呕吐的时候东倒西歪一样。
15 Babu abin da Masar za tă yi, kai ko wutsiya, reshen dabino ko iwa.
埃及中,无论是头与尾, 棕枝与芦苇,所做之工都不成就。
16 A wannan rana Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki lokacin da Ubangiji Maɗaukaki ya ɗaga hannu a kansu.
到那日,埃及人必像妇人一样,他们必因万军之耶和华在埃及以上所抡的手,战兢惧怕。
17 Ƙasar Yahuda kuma za kawo fargaba ga Masarawa; kowanne da Yahuda ya ambace zai firgita, saboda abin da Ubangiji Maɗaukaki yake shiri a kansu.
犹大地必使埃及惊恐,向谁提起犹大地,谁就惧怕。这是因万军之耶和华向埃及所定的旨意。
18 A wannan rana birane biyar a Masar za su yi yaren Kan’ana su kuma miƙa kai cikin yarjejjeniya ga Ubangiji Maɗaukaki. Za a ce da ɗayansu Birnin Hallaka.
当那日,埃及地必有五城的人说迦南的方言,又指着万军之耶和华起誓。有一城必称为“灭亡城”。
19 A wannan rana za a kasance da bagade ga Ubangiji a tsakiyar Masar, da kuma ginshiƙin dutse Ubangiji a iyakarta.
当那日,在埃及地中必有为耶和华筑的一座坛;在埃及的边界上必有为耶和华立的一根柱。
20 Zai zama alama da kuma shaida ga Ubangiji Maɗaukaki a ƙasar Masar. Sa’ad da suka yi kuka ga Ubangiji saboda masu zaluntarsu, zai aiko musu mai ceto da mai kāriya, zai kuma cece su.
这都要在埃及地为万军之耶和华作记号和证据。埃及人因为受人的欺压哀求耶和华,他就差遣一位救主作护卫者,拯救他们。
21 Saboda haka Ubangiji zai sanar da kansa ga Masarawa, kuma a wannan rana za su yarda da Ubangiji. Za su yi masa sujada da hadayu da hadayun hatsi; za su yi alkawura ga Ubangiji su kuma kiyaye su.
耶和华必被埃及人所认识。在那日,埃及人必认识耶和华,也要献祭物和供物敬拜他,并向耶和华许愿还愿。
22 Ubangiji zai bugi Masar da annoba; zai buge su ya kuma warkar da su. Za su juyo wurin Ubangiji, zai amsa roƙonsu ya kuma warkar da su.
耶和华必击打埃及,又击打又医治,埃及人就归向耶和华。他必应允他们的祷告,医治他们。
23 A wannan rana za a kasance da babban hanya daga Masar zuwa Assuriya. Assuriyawa za su tafi Masar, Masarawa kuma za su tafi Assuriya. Masarawa da Assuriyawa za su yi sujada tare.
当那日,必有从埃及通亚述去的大道。亚述人要进入埃及,埃及人也进入亚述;埃及人要与亚述人一同敬拜耶和华。
24 A wannan rana Isra’ila za tă zama na uku, tare da Masar da Assuriya, abin albarka ga duniya.
当那日,以色列必与埃及、亚述三国一律,使地上的人得福;
25 Ubangiji Maɗaukaki zai albarkace su, yana cewa, “Albarka ta tabbata ga Masar, mutanena, Assuriya aikin hannuna, da kuma Isra’ila gādona.”
因为万军之耶和华赐福给他们,说:“埃及—我的百姓,亚述—我手的工作,以色列—我的产业,都有福了!”