< Ishaya 14 >

1 Ubangiji zai yi wa Yaƙub jinƙai; zai sāke zaɓi Isra’ila yă kuma zaunar da su a ƙasarsu. Baƙi ma za su zo su zauna tare da su su haɗa kai da gidan Yaƙub.
[But] Yahweh will act mercifully toward the Israeli people; he will choose [the people of] Israel [to be his people again], and he will allow them to [return here and] live in their own land again. Then people from [many] other countries will come here and unite with the Israeli people.
2 Al’ummai za su ɗauke su su kuma kawo wurin da yake nasu. Gidan Isra’ila kuwa za tă mallaki al’ummai a matsayin bayi maza da mata a ƙasar Ubangiji. Za su mai da waɗanda suka kama su su zama kamammu su kuma yi mulki a kan waɗanda suka taɓa danne su.
People of other nations will help them to return to their [own] land, and those who come from other countries will (work for/become the servants of) the Israeli people. Those who captured people of Israel will be captured by Israeli soldiers, and the people of Israel will rule over the people who [previously] oppressed them.
3 A ranar da Ubangiji ya hutashe ku daga wahala da azaba da muguwar bauta,
Some day Yahweh will free you [Israeli people] from suffering and trouble and from being afraid, and from being cruelly treated as slaves [MTY].
4 za ku yi wa sarkin Babilon wannan ba’a. Mai danniya ya zo ga ƙarshe! Dubi yadda fushinsa ya ƙare!
When that happens, you will make fun of the King of Babylon by saying this: “You treated us cruelly, but that has ended! Your insolently causing others to suffer is finished!
5 Ubangiji ya karye sandar mugaye, sandan mulkin masu mulki,
You evil ruler, Yahweh will get rid of your power, and you will oppress people no longer!
6 wanda cikin fushi ya kashe mutane da bugu marar ƙarewa, kuma cikin fushi ya mamaye al’ummai da fushi ba ƙaƙƙautawa.
You attacked people many times because you were very angry with them, and you subdued/conquered [other] nations by causing them to suffer endlessly.
7 Dukan ƙasashe suna hutawa suna kuma cikin salama; sun ɓarke da waƙa.
[But soon] everything will be quiet and peaceful on the earth. Everyone [PRS] will sing [again]!
8 Har itatuwan fir ma da kuma al’ul na Lebanon suna murna a kanka suna cewa, “Yanzu da aka ƙasƙantar da kai, babu wani mai yankan katakon da ya zo yă yanka mu.”
[It will be as though] even the trees in the forests will joyfully sing this song, the cyprus/pine [trees] and the cedar [trees] in Lebanon will sing it: ‘You (have been overthrown/are no longer a ruler), and now no one comes to get rid of us [MET].’
9 Kabari a ƙarƙashi duk ya shirya don yă sadu da kai a zuwanka; yana tā da ruhohin da suka rasu don su gaishe ka, dukan waɗanda sun taɓa zama shugabanni a duniya; ya sa suka tashi daga kujerun sarauta, dukan waɗanda suke sarakuna a kan al’ummai. (Sheol h7585)
The dead people are [PRS] are eagerly waiting for you to come to the place where they are. The spirits of the world leaders will be delighted to welcome you; those who were kings of many nations [before they died] will stand up [to welcome you]. (Sheol h7585)
10 Duk za su amsa, za su ce maka, “Ashe kai ma raunana ne, kamar mu; ka zama kamar mu.”
They will all shout to you [together], ‘Now you are as weak as we are!’
11 An yi ƙasa da dukan alfarmarka zuwa kabari, tare da surutan garayunka; tsutsotsi sun bazu a ƙarƙashinka tsutsotsi kuma suka rufe ka. (Sheol h7585)
You were very proud and powerful, [but all] that ended when you died, along with the sounds of harps [being played in your palace]. [Now in your grave] maggots will be under you [like a sheet] [MET], and worms will cover you [like a blanket] [MET]. (Sheol h7585)
12 Yaya aka yi ka fāɗo daga sama Ya tauraron safiya, ɗan hasken asuba! An fyaɗa ka da ƙasa, kai da ka taɓa ƙasƙantar da al’ummai!
You have [disappeared from the earth like] [MET] a star which has fallen from the sky; you [were very well-known] [like] [MET] the morning star [which is seen by everyone]; you destroyed [many] nations, but now you have been destroyed.
13 Ka yi tunani a ranka ka ce, “Zan hau zuwa sama; zan ɗaga kursiyina sama da taurarin Allah; zan zauna a kursiyi a kan dutsen taro, a can ƙurewar saman dutse mai tsarki.
You [proudly] said to yourself, ‘I will ascend to heaven, to my throne above God’s stars. I will rule on the mountain where [the gods] gather together, far in the north.
14 Zan haura can bisa gizagizai; zan mai da kaina kamar Mafi Ɗaukaka.”
I will ascend above the clouds and become like the highest/greatest god!’
15 Amma ga shi an gangara da kai zuwa kabari, zuwa zurfafan rami. (Sheol h7585)
[But you were not able to do that]; instead, you were carried down to your grave, and you went to the place where the dead people are. (Sheol h7585)
16 Waɗanda suka gan ka sun zura maka ido, suna tunani abin da zai same ka. “Wannan mutumin ne ya girgiza duniya ya kuma sa mulkoki suka razana,
The [other dead] people there stare at you; they wonder what happened to you. [They say], ‘Is this the man who caused the earth to shake and caused the [people in many] kingdoms to tremble?
17 mutumin da ya mai da duniya ta zama hamada, wanda ya tumɓuke biranenta bai kuma bar kamammunsa suka tafi ba?”
Is this the man who [tried to] cause the world to become a desert, who conquered its cities and did not allow the people whom he captured to return to their homes?’
18 Dukan sarakunan duniya suna kwance a mace, kowa a kabarinsa.
All the kings of the earth [who have died] were greatly honored when they were buried,
19 Amma an jefar da kabarinka kamar reshen da aka ƙi; an rufe ka da waɗanda aka kashe, tare da waɗanda aka soke da takobi, waɗanda suka gangara zuwa duwatsun rami. Kamar gawar da aka tattake da ƙafa,
but your [corpse will] not be buried; it will be thrown away like [SIM] a worthless branch [of a tree]. Your corpse will be under a heap of other corpses of soldiers that were killed by [their enemies’] swords, and [their corpses] were not buried; you will be with those who have gone down to the stony ground in a big pit.
20 ba za a haɗa ka tare da su a jana’iza ba, gama ka hallaka ƙasarka ka kuma kashe mutanenka. Ba za a ƙara ambaci zuriyarka masu aikata mugunta ba.
Your [corpse] will not be buried because you have destroyed your nation and have caused your people to be killed. The descendants of wicked people [like you] will never be honored again.
21 A shirya wuri don a yayyanka’ya’yansa maza saboda zunuban kakanninsu; kada a reno su su gāji ƙasar su cika duniya da biranensu.
[People will say], ‘Slaughter this man’s children because of the sins that their ancestors committed! Do not allow them to become rulers and conquer [all the nations in] the world, and fill the world with the cities [that they rule]!’”
22 “Zan yi gāba da su,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kau da sunan Babilon da waɗanda suka rage da rai a cikinta,’ya’yanta da zuriyarta,” in ji Ubangiji.
[This is what] the Commander of the armies of angels says: “I [myself] will cause Babylon to be conquered. I will get rid of Babylon and its people and their descendants.
23 “Zan mai da ita wuri domin mujiyoyi da kuma fadama; zan share ta da tsintsiyar hallaka,” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
I will cause Babylon to be a place where owls live, a place full of swamps; I will get rid of it completely [as though] [MET] I were sweeping it with a broom. [That is what I], the Commander of the armies of angels, say.”
24 Ubangiji Maɗaukaki ya rantse, “Tabbatacce, kamar yadda na riga na shirya, haka zai kasance, kuma kamar yadda na nufa, haka zai zama.
The Commander of the armies of angels has [also] solemnly promised this: “The things that I have planned will surely happen [DOU].
25 Zan ragargazar da Assuriya a cikin ƙasata; a kan duwatsuna zan tattake shi. Za a ɗauke nauyin da ya sa wa mutanena, a kuma ɗauke nauyinsa daga kafaɗunsu.”
[When the army of] Assyria is in my land [of Israel], I will crush them. [It will be as though] I will trample them on my mountains. My people will no longer be the slaves [MET] of the people of Assyria; [it will be as though] [MET] I will take away the burdens that are on their shoulders.
26 Wannan shi ne shirin da na yi domin dukan duniya; wannan shi ne hannun da aka miƙa a bisa dukan al’ummai ke nan.
I have a plan for everyone on the earth, a plan to show my power [MTY] to punish all the nations.
27 Gama Ubangiji Maɗaukaki ya ƙudura ya yi wannan, wa kuwa zai hana shi? Ya riga ya miƙa hannunsa, wa zai komar da shi?
[I], the Commander of the armies of angels, have spoken, and no one can [RHQ] change my mind. When I raise my fist [to strike Assyria], no one [RHQ] will be able to stop me [from doing that].”
28 Wannan abin da Allah ya yi magana ya zo ne a shekarar da Sarki Ahaz ya mutu.
I received this message [from Yahweh] during the year that King Ahaz died:
29 Kada ku yi farin ciki, dukanku Filistiyawa, cewa sandar da ta buge ku ta karye; daga saiwar wannan maciji wani mugun maciji mai dafi zai taso,’ya’yansa za su zama wani maciji masu dafi mai tashi sama.
You people of Philistia, do not rejoice that the enemy army [MET] that attacked you has been defeated and that their king is dead. He was [as dangerous as] [MET] a snake, but there will be another king, who will be more [dangerous] than a cobra; he will be [like] [MET] a quick-moving poisonous snake.
30 Mafi talauci na matalauta zai sami wurin kiwo, mabukata kuma za su kwana lafiya. Amma zan hallakar da saiwarka da matsananciyar yunwa; za tă kashe naka da suka rage da rai.
Those of my people who are very poor will take care of their flocks of sheep, and the needy people will lie down safely, but I will cause you people [of Philistia] who are still alive [DOU] to die from famine.
31 Ki yi ihu, ya ke ƙofa! Yi kururuwa, ya ke birni! Ku razana, dukanku Filistiyawa! Ƙunshin hayaƙi yana tasowa daga arewa, kuma babu matsorata a cikin sojojinsa.
[So], you people of Philistia, wail at the gates of your cities! You should be extremely afraid, because [a very powerful army] will come from the north [to attack you]; [their chariots will stir up the dust like] [MET] a cloud of smoke. Each of their soldiers is ready to fight.
32 Wace amsa ce za a bayar wa jakadun wannan al’umma? “Ubangiji ya kafa Sihiyona, kuma a cikinta mutanensa masu shan azaba za su sami mafaka.”
If messengers [from Philistia] come to us [Israeli people], this is what we must [RHQ] tell them: “Yahweh has established Jerusalem, [not Philistia], and his people who are oppressed will be safe inside [the walls of] Jerusalem.”

< Ishaya 14 >