< Ishaya 11 >
1 Toho zai fito daga kututturen Yesse; daga saiwarsa Reshe zai ba da’ya’ya.
Et il sortira un rejeton de la racine de Jessé, et de cette racine une fleur naîtra;
2 Ruhun Ubangiji zai kasance a kansa, Ruhun hikima da na fahimta, Ruhun shawara da na iko, Ruhun sani da na tsoron Ubangiji,
Et sur lui reposera l'Esprit de Dieu, l'esprit de sagesse et d'intelligence, l'esprit de conseil et de force, l'esprit de science et de piété;
3 zai kuwa ji daɗin tsoron Ubangiji. Ba zai yi hukunci ta wurin abin da ya gani da idanunsa ba, ba zai kuwa yanke shawara ta wurin abin da ya ji da kunnuwansa ba;
L'esprit de crainte du Seigneur le remplira. Il ne jugera pas selon la gloire; il ne condamnera point selon la rumeur commune.
4 amma da adalci zai yi wa masu bukata shari’a, da gaskiya zai yanke shawarwari saboda matalautan duniya. Kamar sanda zai bugi duniya da maganar bakinsa; da numfashin leɓunansa zai yanke mugaye.
Mais il rendra justice aux humbles, et il relèvera les humbles de la terre; il frappera la terre d'une parole de sa bouche, et d'un souffle de ses lèvres il détruira les impies.
5 Adalci ne zai zama abin ɗamararsa aminci kuma igiyar da zai ɗaura kewaye da gindinsa.
Il se ceindra les reins de justice, et il revêtira ses flancs de vérité.
6 Kyarkeci zai zauna tare da ɗan rago damisa za tă kwanta tare da akuya, ɗan maraƙi da zaki da ɗan saniya za su yi kiwo tare; ɗan yaro ne zai lura da su.
Et le loup broutera avec l'agneau; et la panthère se reposera avec la chèvre; et le bœuf, le taureau et le lion brouteront ensemble; et un petit enfant les conduira.
7 Saniya da beyar za su yi kiwo tare, ƙananansu za su kwanta tare, zaki kuma zai ci ciyawa kamar saniya.
Ensemble brouteront l'ours et la génisse, ensemble seront leurs petits; et le lion se nourrira de paille comme le bœuf;
8 Jariri zai yi wasa kurkusa da ramin gamsheƙa, ɗan yaro kuma zai sa hannunsa a ramin maciji mai mugun dafi.
Et l'enfant au berceau mettra sa main dans les trous des aspics, dans le nid même de leurs petits.
9 Ba za su yi lahani ko su hallaka wani a dutsena mai tsarki ba, gama duniya za tă cika da sanin Ubangiji kamar yadda ruwaye suka rufe teku.
Et ils ne lui feront aucun mal, et ils ne pourront nuire à aucun des miens sur ma montagne sainte; car l'univers est plein de la connaissance du Seigneur, comme les eaux couvrent la mer.
10 A wannan rana Saiwar Yesse zai miƙe kamar tuta don mutanenta; al’ummai za su tattaru wurinsa, wurin hutunsa kuma zai zama mai daraja.
Et en ce jour apparaîtra la racine de Jessé et celui qui s'élèvera pour régner sur les nations, et les nations espèreront en lui, et sa mort fera sa gloire.
11 A wannan rana Ubangiji zai miƙa hannunsa sau na biyu don yă maido da raguwar da ta rage na mutanensa daga Assuriya, daga Masar ta Ƙasa, daga Masar ta Bisa, daga Kush, daga Elam, daga Babiloniya, daga Hamat da kuma daga tsibiran teku.
Et en ce jour le Seigneur montrera encore sa main, et il montrera son zèle pour les restes de son peuple, échappés aux Assyriens, à l'Égypte, à Babylone, aux Éthiopiens, aux Élamites, aux peuples du Levant et aux Arabes.
12 Zai tā da tuta saboda al’ummai yă kuma tattara masu zaman bauta na Isra’ila; zai tattara mutanen Yahuda da suke a warwatse kusurwoyi huɗu na duniya.
Et il élèvera son étendard sur les nations, et il rassemblera les égarés d'Israël, les dispersés de Juda, et il les réunira des quatre ailes de la terre.
13 Kishin Efraim zai ɓace, za a kuma kau da abokan gāban Yahuda; Efraim ba zai yi kishin Yahuda ba, haka ma Yahuda ba zai yi gāba da Efraim ba.
Et la jalousie d'Éphraïm sera détruite, et les ennemis de Juda périront; Éphraïm ne portera plus envie à Juda, et Juda n'affligera plus Éphraïm.
14 Tare za su fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi daga yamma; tare za su washe mutane wajen gabas. Za su ɗibiya hannuwa a kan Edom da Mowab, Ammonawa kuma za su yi musu biyayya.
Ils voleront sur les eaux dans les barques des Philistins; ils se feront une proie des peuples de la mer, de ceux de l'Orient et de l'Idumée, et d'abord ils mettront la main sur Moab; mais les fils d'Ammon seront les premiers soumis.
15 Ubangiji zai busar da bakin tekun Masar; da iska mai zafi zai share hannunsa a bisa Kogin Yuferites Zai rarraba shi yă zama ƙanana rafuffuka bakwai saboda mutane su iya hayewa da ƙafa.
Et le Seigneur désolera la mer d'Égypte, et au milieu d'une violente tempête il fera tomber son bras sur le fleuve, et il en frappera les sept bouches, de sorte qu'on les traversera avec des sandales.
16 Za a yi babbar hanya saboda raguwa mutanensa da ta rage daga Assuriya, kamar yadda ta kasance wa Isra’ila sa’ad da suka fito daga Masar.
Et ce sera un passage pour mon peuple resté en Égypte, et il arrivera à Israël comme au temps où il sortit de la terre d'Égypte.