< Hosiya 9 >

1 Kada ku yi farin ciki, ya Isra’ila; kada ku yi murna kamar waɗansu al’ummai. Gama kun yi rashin aminci ga Allahnku; kuna son hakkokin karuwa a kowace masussuka.
Ne te livre pas à la joie, Israël, à l'allégresse comme les peuples; car tu t'es prostitué loin de ton Dieu, tu as aimé le salaire de la prostituée, sur toutes les aires à blé.
2 Masussukai da wuraren matsin inabi ba za su ciyar da mutane ba; sabon ruwan inabi zai kāsa musu.
Ni l'aire ni la cuve ne les nourriront, et le vin nouveau les reniera.
3 Ba za su ci gaba da zama a ƙasar Ubangiji ba; Efraim zai koma Masar yă kuma ci abinci marar tsarki a Assuriya.
Ils n'habiteront pas dans la terre de Yahweh; Ephraïm retournera en Egypte, et ils mangeront en Assyrie des aliments impurs.
4 Ba za su zuba hadayun ruwan inabi ga Ubangiji ba, ba kuwa hadayunsu za su gamshe shi ba. Irin hadayun nan za su zama musu kamar burodin masu makoki; duk wanda ya ci su zai ƙazantu. Wannan abincin zai zama na kansu ne; ba zai zo cikin haikalin Ubangiji ba.
Ils ne feront pas à Yahweh des libations de vin, et leurs sacrifices ne lui seront pas agréables; ce sera pour eux comme un pain de deuil, ceux qui en mangeront se rendront impurs; car leur pain sera pour eux-mêmes, il n'entrera pas dans la maison de Yahweh.
5 Me za ku yi a ƙayyadaddiyar ranar bukukkuwarku, a ranakun bikin Ubangiji?
Que ferez-vous au jour de solennité, au jour de la fête de Yahweh?
6 Ko da sun kuɓuta daga hallaka, Masar za tă tattara su, Memfis kuma za tă binne su. Sarƙaƙƙiya za tă mamaye kayan azurfansu, ƙayayyuwa su tsiro a cikin tentunansu.
Car voici qu'ils sont partis devant la dévastation, l'Egypte les recueillera. Memphis les ensevelira; leurs objets précieux d'argent, le chardon s'en emparera; l'épine envahira leurs tentes.
7 Kwanakin hukunci suna zuwa, kwanakin ba da lissafi suna a kusa. Bari Isra’ila su san da wannan. Saboda zunubanku sun yi yawa ƙiyayyarku kuma ta yi yawa, har ake ɗauka annabi wawa ne, mutumin da aka iza kuwa mahaukaci.
Ils sont venus les jours du châtiment! ils sont venus les jours de la rétribution! Israël va le savoir. Le prophète est fou, l'homme de l'esprit est en délire! A cause de la grandeur de ton iniquité, et de ta grande hostilité.
8 Annabi, tare da Allahna, su ne masu tsaro a bisa Efraim, duk da haka tarko na jiransa a dukan hanyoyi, da kuma ƙiyayya a cikin gidan Allahnsa.
La sentinelle d'Ephraïm est avec mon Dieu; le prophète trouve un filet d'oiseleur sur toutes ses voies, la persécution dans la maison de son Dieu.
9 Sun nutse da zurfi cikin lalaci, kamar a kwanakin Gibeya. Allah zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta su saboda zunubansu.
Ils sont corrompus jusqu'au fond, comme aux jours de Gabaa; Yahweh se souviendra de leur iniquité, il punira leurs péchés.
10 “Sa’ad da na sami Isra’ila, ya zama kamar samun inabi a hamada; sa’ad da na ga kakanninku, ya zama kamar ganin’ya’yan itace na farko a itacen ɓaure. Amma sa’ad da suka zo Ba’al-Feyor, suka keɓe kansu wa gumaka bankunya sai suka zama abubuwan banƙyama kamar abubuwan da suke ƙauna.
Comme des raisins dans le désert, j'ai trouvé Israël; comme une primeur sur un jeune figuier, j'ai vu vos pères. Mais eux sont arrivés à Béelphégor; ils se sont consacrés à l'idole infâme, et sont devenus abominables comme l'objet de leur amour.
11 Darajar Efraim za tă yi firiya tă tafi kamar tsuntsu, ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki.
La gloire d'Ephraïm s'envolera comme un oiseau; plus d'enfantement, plus de grossesse, plus de conception.
12 Ko da sun yi renon’ya’ya, zan sa su yi baƙin cikin kowannensu. Kaitonsu sa’ad da na juya musu baya!
Lors même qu'ils élèveraient leurs enfants, je les en priverai avant qu'ils soient devenus hommes; car malheur à eux aussi, si je me retire d'eux!
13 Na ga Efraim, kamar birnin Taya, da aka kafa a wuri mai daɗi. Amma Efraim zai fitar da’ya’yansu ga masu yanka.”
Ephraïm, quand je porte mon regard du côté de Tyr, est planté dans une belle prairie; et Ephraïm va mener ses enfants à l'égorgeur!
14 Ka ba su, ya Ubangiji Me za ka ba su? Ka ba su mahaifar da za su yi ɓarin ciki da busassun nono.
Donne-leur, Yahweh... que leur donneras-tu?... Donne-leur un sein stérile, et des mamelles desséchées.
15 “Saboda dukan muguntarsu a Gilgal, na ƙi su a can. Saboda ayyukansu na zunubi, zan kore su daga gidana. Ba zan ƙara ƙaunace su ba; dukan shugabanninsu’yan tawaye ne.
Toute leur malice est a Galgal, car c'est là que je les ai pris en haine. A cause de la méchanceté de leurs actions, je les chasserai de ma maison; je n'aurai plus d'amour pour eux: tous leurs chefs sont des rebelles.
16 An ka da Efraim, saiwarsu ta bushe, ba sa ba da amfani. Ko da sun haifi’ya’ya zan kashe waɗanda suka fi ƙauna.”
Ephraïm est frappé; sa racine est desséchée, ils ne porteront pas de fruit. Et si même ils enfantent, je ferai périr les fruits chéris de leurs entrailles.
17 Allahna zai ƙi su saboda ba su yi masa biyayya ba; za su zama masu yawo a cikin al’ummai.
Mon Dieu les rejettera, parce qu'ils ne l'ont pas écouté, et ils seront errants parmi les nations.

< Hosiya 9 >