< Hosiya 9 >

1 Kada ku yi farin ciki, ya Isra’ila; kada ku yi murna kamar waɗansu al’ummai. Gama kun yi rashin aminci ga Allahnku; kuna son hakkokin karuwa a kowace masussuka.
Rejoice not too loudly, Israel, like the nations, for you have commited adultery, being untrue to your God. You have loved a prostitute’s wages on every threshing floor.
2 Masussukai da wuraren matsin inabi ba za su ciyar da mutane ba; sabon ruwan inabi zai kāsa musu.
Threshing floor and wine vat won’t feed them, the new wine will fail them.
3 Ba za su ci gaba da zama a ƙasar Ubangiji ba; Efraim zai koma Masar yă kuma ci abinci marar tsarki a Assuriya.
They will not stay in the Lord’s land, but Ephraim will return to Egypt, and in Assyria they will eat what is unclean.
4 Ba za su zuba hadayun ruwan inabi ga Ubangiji ba, ba kuwa hadayunsu za su gamshe shi ba. Irin hadayun nan za su zama musu kamar burodin masu makoki; duk wanda ya ci su zai ƙazantu. Wannan abincin zai zama na kansu ne; ba zai zo cikin haikalin Ubangiji ba.
They will not pour out libations of wine to the Lord, nor please him with their sacrifices. Their bread will be like the bread of mourners: all who eat it will defile themselves. For their bread will be only for their hunger, it will not come into the Lord’s temple.
5 Me za ku yi a ƙayyadaddiyar ranar bukukkuwarku, a ranakun bikin Ubangiji?
What will you do on the day of the festival? Or on the day of the Lord’s feast?
6 Ko da sun kuɓuta daga hallaka, Masar za tă tattara su, Memfis kuma za tă binne su. Sarƙaƙƙiya za tă mamaye kayan azurfansu, ƙayayyuwa su tsiro a cikin tentunansu.
Even if they flee from destruction, Egypt will gather them, Memphis will bury them. Nettles will take possession of their treasure of silver, thorns will push into their tents.
7 Kwanakin hukunci suna zuwa, kwanakin ba da lissafi suna a kusa. Bari Isra’ila su san da wannan. Saboda zunubanku sun yi yawa ƙiyayyarku kuma ta yi yawa, har ake ɗauka annabi wawa ne, mutumin da aka iza kuwa mahaukaci.
The days of punishment are come, the days of recompense are at hand, as soon the Israelites will know! ‘The prophet is a fool, the inspired man is raving mad!’ It is because of the greatness of your iniquity and the greatness of your hatred.
8 Annabi, tare da Allahna, su ne masu tsaro a bisa Efraim, duk da haka tarko na jiransa a dukan hanyoyi, da kuma ƙiyayya a cikin gidan Allahnsa.
Ephraim acts the spy with my God, a prophet finds the snares of a fowler are in all his ways. In the house of his God they lay hostile plots,
9 Sun nutse da zurfi cikin lalaci, kamar a kwanakin Gibeya. Allah zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta su saboda zunubansu.
they commit crimes as in the days of Gibeah, God will remember their iniquity. He will punish their sin.
10 “Sa’ad da na sami Isra’ila, ya zama kamar samun inabi a hamada; sa’ad da na ga kakanninku, ya zama kamar ganin’ya’yan itace na farko a itacen ɓaure. Amma sa’ad da suka zo Ba’al-Feyor, suka keɓe kansu wa gumaka bankunya sai suka zama abubuwan banƙyama kamar abubuwan da suke ƙauna.
I found Israel like finding grapes in the wilderness. I saw your ancestors like they were the first fruit on a fig tree, but as soon as they came to Baal-peor, they consecrated themselves to shamefulness, and became as abominable as the object of their love.
11 Darajar Efraim za tă yi firiya tă tafi kamar tsuntsu, ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki.
Ephraim – like a bird his glory flies away. There will be no more birth, no more motherhood, no more conception.
12 Ko da sun yi renon’ya’ya, zan sa su yi baƙin cikin kowannensu. Kaitonsu sa’ad da na juya musu baya!
Even though they bring up their children, I will bereave them until not one is left. Woe to them when I turn away from them!
13 Na ga Efraim, kamar birnin Taya, da aka kafa a wuri mai daɗi. Amma Efraim zai fitar da’ya’yansu ga masu yanka.”
Ephraim – planted like Tyre in a meadow, But Ephraim too must lead forth their children to slaughter.
14 Ka ba su, ya Ubangiji Me za ka ba su? Ka ba su mahaifar da za su yi ɓarin ciki da busassun nono.
Give them, Lord – what will you give? Give them a miscarrying womb and shrivelled up breasts!
15 “Saboda dukan muguntarsu a Gilgal, na ƙi su a can. Saboda ayyukansu na zunubi, zan kore su daga gidana. Ba zan ƙara ƙaunace su ba; dukan shugabanninsu’yan tawaye ne.
All their evil began in Gilgal, there I learned to hate them. Because of the evil of their deeds I will drive them out of my house. I will no longer love them, for all their princes are rebels.
16 An ka da Efraim, saiwarsu ta bushe, ba sa ba da amfani. Ko da sun haifi’ya’ya zan kashe waɗanda suka fi ƙauna.”
Ephraim is blighted, their root withered. If they do bear children, I will slay the darlings of their womb,
17 Allahna zai ƙi su saboda ba su yi masa biyayya ba; za su zama masu yawo a cikin al’ummai.
My God will reject them because they have not listened to him, and they will become wanderers among the nations.

< Hosiya 9 >