< Hosiya 7 >

1 a duka sa’ad da zan warkar da Isra’ila, zunuban Efraim za su tonu za a kuma bayyana laifofin Samariya. Suna ruɗu, ɓarayi sukan fasa su shiga gidaje,’yan fashi sukan yi fashi a tituna;
Ko sem hotel ozdraviti Izraela, takrat je bila odkrita krivičnost Efrájima in zlobnost Samarije, kajti zagrešili so neresnico. In tat vstopa in krdelo roparjev pleni zunaj.
2 amma ba su gane cewa na tuna da dukan ayyukan muguntarsu ba. Zunubansu sun kewaye su; kullum suna a gabana.
V svojih srcih pa ne preudarijo, da se spominjam vse njihove zlobnosti. Sedaj so jih njihova lastna dejanja obkrožila; pred mojim obrazom so.
3 “Suna faranta wa sarki zuciya da muguntarsu, shugabanni kuma da ƙarairayinsu.
Kralja razveseljujejo s svojo zlobnostjo in prince s svojimi lažmi.
4 Dukansu mazinata ne suna ƙuna kamar matoya wadda mai gashin burodi ba ya bukata yă tura mata wuta daga cuɗe kullu har kumburinsa.
Vsi so zakonolomci, kakor peč, ki jo segreje pek, ki preneha kuriti, potem ko je pregnetel testo, dokler to ni vzhajano.
5 A ranar bikin sarkinmu shugabanni sukan bugu da ruwan inabi, yă yi cuɗanya da masu ba’a.
Na dan našega kralja so ga princi naredili bolnega z vinskimi mehovi; svojo roko podaja s posmehljivci.
6 Zukatansu suna kamar matoya; sukan kusace shi da wayo. Muguwar aniyarsu takan yi ta ci dukan dare; da safe sai ta ƙuna kamar harshen wuta.
Kajti svoje srce so pripravili kakor peč, medtem ko prežijo v zasedi. Njihov pek spi vso noč; zjutraj ta gori kakor plameneč ogenj.
7 Dukansu suna da zafi kamar matoya; suna kashe masu mulkinsu. Dukan sarakunansu sukan fāɗi, kuma babu waninsu da yake kira gare ni.
Vsi so vroči kakor peč in požrli so svoje sodnike; vsi njihovi kralji so padli; tam ni nobenega izmed njih, ki kliče k meni.
8 “Efraim yana cuɗanya da al’ummai; Efraim waina ne mai fāɗi da ba a juye ba.
Efrájim se je pomešal med ljudstvo, Efrájim je neobrnjen kolač.
9 Baƙi sun tsotse ƙarfinsa, amma bai gane ba. Gashi kansa ya cika da furfura, amma bai lura ba.
Tujci so požrli njegovo moč, on pa tega ne spoznava. Da, sivi lasje so tu in tam na njem, vendar ne spoznava.
10 Girmankan Isra’ila ya ba da shaida a kansa, amma duk da haka bai dawo ga Ubangiji Allahnsa ko yă neme shi ba.
Izraelov ponos pričuje v njegov obraz, oni pa se ne vrnejo h Gospodu, svojemu Bogu niti ga zaradi vsega tega ne iščejo.
11 “Efraim yana kama da kurciya, marar wayo, marar hankali, yanzu yana kira ga Masar, yanzu yana juyewa ga Assuriya.
Tudi Efrájim je podoben neumni golobici brez srca; kličejo k Egiptu, hodijo v Asirijo.
12 Sa’ad da suka tafi, zan jefa ragata a kansu; zai janye su ƙasa kamar tsuntsayen sararin sama. Sa’ad da na ji suna tafiya tare, zan kama su.
Ko bodo šli, bom nadnje razširil svojo mrežo. Sklatil jih bom dol kakor perjad neba, kaznoval jih bom, kakor je slišala njihova skupnost.
13 Kaitonsu, domin sun kauce daga gare ni! Hallaka za tă aukar musu, domin sun tayar mini! Na ƙudura in cece su amma suna faɗar ƙarya a kaina.
Gorje jim! Kajti zbežali so od mene. Naj jim bo namenjeno uničenje! Ker so se prekršili zoper mene. Čeprav sem jih odkupil, so oni kljub temu zoper mene govorili laži.
14 Ba sa yin mini kuka da zuciyarsu amma suna ihu a kan gadajensu. Sukan taru wurin ɗaya don hatsi da ruwan inabi amma su juya mini baya.
In niso klicali k meni s svojim srcem, ko so tulili na svojih posteljah; zbrali so se zaradi žita in vina in se uprli zoper mene.
15 Na horar da su na kuma ƙarfafa su, amma sun ƙulla mini maƙarƙashiya.
Čeprav sem utrdil in okrepil njihove lakte, so zoper mene še vedno domišljali vragolijo.
16 Ba sa juya ga Mafi Ɗaukaka; suna kama da tanƙwararren baka. Za a kashe shugabanninsu da takobi saboda banzan maganganunsu. Saboda wannan za a wulaƙanta su a ƙasar Masar.
Vračajo se, toda ne k Najvišjemu; so kot varljiv lok; njihovi princi bodo padli pod mečem zaradi besa njihovega jezika. To bo v njihov posmeh v egiptovski deželi.

< Hosiya 7 >