< Hosiya 6 >
1 “Ku zo, mu koma ga Ubangiji. Ya yayyage mu kucu-kucu amma zai warkar da mu; ya ji mana ciwo amma zai daure mana miyakunmu.
Venez, retournons à l'Éternel! Car il a déchiré, mais il nous guérira; il a frappé, mais il bandera nos plaies. Il nous rendra la vie dans deux jours.
2 Bayan kwana biyu zai rayar da mu, a rana ta uku zai tashe mu, don mu rayu a gabansa.
Le troisième jour il nous relèvera, et nous vivrons en sa présence.
3 Bari mu yarda da Ubangiji; bari mu nace gaba don mu yarda da shi. Muddin rana tana fitowa, zai bayyana; zai zo mana kamar ruwan bazara, kamar ruwan saman farko da yake jiƙe ƙasa.”
Et nous connaîtrons l'Éternel, nous nous attacherons à le connaître. Son lever se prépare comme celui de l'aurore, et il viendra à nous comme la pluie, comme la pluie de l'arrière-saison, qui arrose la terre.
4 “Me zan yi da kai Efraim? Me zan yi da kai Yahuda? Ƙaunarku tana kamar hazon safiya, kamar raɓar safiya da takan ɓace.
Que te ferai-je, Éphraïm? Que te ferai-je, Juda? Votre piété est comme la nuée du matin, comme la rosée qui dès le matin se dissipe.
5 Saboda haka na yayyaga ku kucu-kucu tare da annabawana, na kashe ku da kalmomin bakina; hukuntaina sun haskaka kamar walƙiya a kanku.
C'est pourquoi je les frappe par les prophètes, je les tue par les paroles de ma bouche, et mes jugements éclateront comme la lumière.
6 Gama jinƙai nake bukata, ba hadaya ba, ku kuma san Allah a maimakon hadayun ƙonawa.
Car c'est la piété que j'aime et non le sacrifice, et la connaissance de Dieu plus que les holocaustes.
7 Kamar Adamu, sun tā da alkawari, sun yi mini rashin aminci a can.
Mais comme Adam ils ont transgressé l'alliance; là ils ont agi perfidement contre moi.
8 Gileyad birni ce ta mugayen mutane, da tabon alamun jini.
Galaad est une ville d'ouvriers d'iniquité, pleine de traces de sang.
9 Kamar yadda mafasa sukan yi fakon mutum, haka ƙungiyoyin firistoci suke; suna kisa a hanya zuwa Shekem, suna aikata laifofi bankunya.
Et la troupe des sacrificateurs est comme les bandes qui épient les gens, et qui massacrent sur le chemin de Sichem; car ils commettent le crime.
10 Na ga wani abu mai bantsoro a gidan Isra’ila. A can Efraim ya miƙa wuya ga karuwanci Isra’ila kuma ta ƙazantu.
Dans la maison d'Israël, j'ai vu une chose horrible: là est la prostitution d'Éphraïm; là Israël se souille!
11 “Ku kuma, ya mutanen Yahuda, na shirya muku ranar girbi. “A duk sa’ad da zan mayar da dukiya wa mutanena,
Pour toi aussi, Juda, une moisson est réservée, quand je ramènerai les captifs de mon peuple.