< Hosiya 3 >

1 Ubangiji ya ce mini, “Ka tafi, ka sāke nuna wa matarka ƙauna, ko da yake wani yana son ta, ita kuma mazinaciya ce. Ka ƙaunace ta yadda Ubangiji yake ƙaunar Isra’ilawa, ko da yake sun juya ga waɗansu alloli suna kuma ƙauna wainar zabibi mai tsarki.”
And YHWH says to me: “Again, go, love a woman, loved of a friend, and an adulteress, like the loved of YHWH, the sons of Israel, and they are turning to other gods, and are lovers of grape-cakes.”
2 Ta haka na saye ta da shekel goma sha biyar na azurfa da kuma wajen buhu na sha’ir.
And I buy her for myself for fifteen pieces of silver, and a homer and a lethech of barley;
3 Sai na faɗa mata, “Za ki zauna tare da ni kwanaki masu yawa; kada ki yi karuwanci ko ki yi abuta da wani namiji, ni kuwa zan zauna tare da ke.”
and I say to her, “You remain many days for Me, you do not go whoring, nor become anyone’s; and I also [am] for you.”
4 Gama Isra’ilawa za su yi kwanaki masu yawa ba tare da sarki ko shugaba ba, babu hadaya ko keɓaɓɓun duwatsu, babu efod ko gunki.
For the sons of Israel remain without a king for many days, and there is no prince, and there is no sacrifice, and there is no standing pillar, and there is no ephod and teraphim.
5 Daga baya Isra’ilawa za su dawo su nemi Ubangiji Allahnsu da kuma Dawuda sarkinsu. Za su je da rawan jiki wajen Ubangiji da kuma ga albarkunsa a kwanakin ƙarshe.
Afterward the sons of Israel have turned back, and sought their God YHWH, and David their king, and have hurried to YHWH, and to His goodness, in the latter end of the days.

< Hosiya 3 >