< Hosiya 2 >
1 “Ka ce da’yan’uwanka maza, ‘Mutanena,’ ka kuma ce da’yan’uwanka mata, ‘Ƙaunatacciyata.’
Dites à vos frères: Ammi (mon peuple)! et à vos sœurs: Ruchama (dont on a pitié)!
2 “Ka tsawata wa mahaifiyarka, ka tsawata mata, gama ita ba matata ba ce, ni kuma ba mijinta ba ne. Ku roƙe ta tă daina karuwancinta da kuma rashin aminci a tsakanin nononta.
Plaidez contre votre mère, plaidez! Car elle n'est pas ma femme, et je ne suis point son mari. Qu'elle ôte ses prostitutions de son visage et ses adultères de son sein;
3 In ba haka ba zai tuɓe ta tsirara in bar ta kamar yadda take a ranar da aka haife ta; zan sa ta zama kamar hamada, in mayar da ita busasshiyar ƙasar, in kashe ta da ƙishirwa.
De peur que je ne la dépouille à nu, et que je ne la mette comme au jour de sa naissance, et que je ne la rende semblable à un désert, à une terre aride, et ne la fasse mourir de soif;
4 Ba zan nuna wa’ya’yanta ƙaunata ba, domin su’ya’yan zina ne.
Et que je n'aie point pitié de ses enfants, parce que ce sont des enfants de prostitution.
5 Mahaifiyarsu ta yi rashin aminci ta kuma ɗauki cikinsu ta wurin yi abin kunya. Ta ce, ‘Zan bi kwartayena, waɗanda suke ba ni abinci da ruwa, ulu nawa da lilina, mai nawa da kuma abin sha na.’
Car leur mère s'est prostituée, celle qui les a conçus s'est déshonorée; car elle a dit: “J'irai après mes amants, qui me donnent mon pain et mon eau, ma laine et mon lin, mon huile et mon breuvage. “
6 Saboda haka zai tare hanyarta da ƙaya; zan yi mata katanga don kada tă sami hanya.
C'est pourquoi, voici, je vais fermer ton chemin avec des épines. J'y élèverai un mur, tellement qu'elle ne trouvera plus ses sentiers.
7 Za tă bi kwartayenta amma ba za tă kama su ba; za tă neme su amma ba za tă same su ba. Sa’an nan za tă ce, ‘Zan koma ga mijina na fari, gama dā ya fi mini yadda nake a yanzu.’
Elle poursuivra ses amants, et elle ne les atteindra pas; elle les cherchera, mais elle ne les trouvera point. Puis elle dira: “J'irai, et je retournerai à mon premier mari; car alors j'étais mieux que je ne suis maintenant. “
8 Ba ta yarda cewa ni ne wanda ya ba ta hatsi, sabon ruwan inabi da mai ba, wanda ya jibge mata azurfa da zinariya, waɗanda suka yi amfani wa Ba’al ba.
Or elle n'a pas reconnu que c'était moi qui lui donnais le froment, et le moût, et l'huile, et qui lui multipliais l'argent et l'or, dont ils faisaient un Baal.
9 “Saboda haka zan ƙwace hatsina sa’ad da ya nuna, da sabon ruwan inabina sa’ad da ya ƙosa. Zan karɓe ulu nawa da lilina, da take niyya ta rufe tsiraicinta.
C'est pourquoi je reprendrai mon froment en son temps, et mon moût en sa saison, et j'enlèverai ma laine et mon lin qui couvraient sa nudité.
10 Saboda haka yanzu zan buɗe tsiraicinta a idanun kwartayenta; ba wani da zai ƙwace ta daga hannuwana.
Et je découvrirai maintenant sa turpitude aux yeux de ses amants, et nul ne la délivrera de ma main.
11 Zan tsayar da dukan bukukkuwarta, bukukkuwarta na shekara-shekara, da kuma kiyaye bikin Sababbin Wata nata, kwanakin Asabbacinta, dukan ƙayyadaddun bukukkuwarta.
Je ferai cesser toute sa joie, ses fêtes, ses nouvelles lunes, ses sabbats et toutes ses solennités.
12 Zan lalatar da inabinta da kuma itatuwan ɓaurenta, waɗanda take cewa su ne abin da kwartayenta suka biya; zan mayar da su kurmi, namun jeji kuwa za su ci su.
Je dévasterai ses vignes et ses figuiers, dont elle a dit: “Ce sont là mes salaires, que mes amants m'ont donnés. “Je les réduirai en forêt, et les bêtes des champs les dévoreront.
13 Zan hukunta ta saboda kwanakin da ta ƙone turare wa Ba’al; ta yi wa kanta ado da zobai da duwatsu masu daraja, ta bi kwartayenta, amma ta manta da ni,” in ji Ubangiji.
Et je la punirai pour les jours où elle offrait des parfums aux Baals, en se parant de ses bagues et de ses joyaux, et s'en allait après ses amants, et m'oubliait, dit l'Éternel.
14 “Saboda haka yanzu zan rarrashe ta; zan bishe ta zuwa hamada in kuma yi mata magana a hankali.
C'est pourquoi, voici, je l'attirerai, et je la ferai aller au désert, et je parlerai à son cœur.
15 A can zan mayar mata da gonakin inabinta, zan kuma sa Kwarin Akor yă zama ƙofar bege. A can za tă rera kamar a kwanakin ƙuruciyarta, kamar a lokacin da ta fita daga Masar.
Et de là je lui donnerai ses vignes, et la vallée d'Acor, comme une entrée d'espérance; et elle y chantera comme au temps de sa jeunesse, comme au jour où elle remonta du pays d'Égypte.
16 “A waccan rana,” in ji Ubangiji, “za ki ce da ni ‘mijina’; ba za ki ƙara ce ni ‘maigidana’ ba.
Et il arrivera en ce jour-là, dit l'Éternel, que tu m'appelleras: “Mon mari; “et tu ne m'appelleras plus: “Mon Baal (maître). “
17 Zan cire sunayen Ba’al daga leɓunanta; ba za a ƙara kira sunayensu ba.
Et j'ôterai de sa bouche les noms des Baals; et on ne fera plus mention de leur nom.
18 A waccan rana zan yi alkawari dominsu da namun jeji da kuma tsuntsayen sararin sama da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa. Baka da takobi da yaƙi zan sa su ƙare a ƙasar, domin duk su zauna lafiya.
En ce jour-là, je traiterai pour eux une alliance avec les bêtes des champs, avec les oiseaux des cieux et les reptiles de la terre; je briserai, j'ôterai du pays l'arc, l'épée et la guerre, et je les ferai reposer en sûreté.
19 Zan ɗaura aure da ke har abada; zan ɗaura aure da yake cikin adalci da gaskiya, cikin ƙauna da jinƙai.
Et je t'épouserai pour toujours; je t'épouserai par une alliance de justice et de droit, de bonté et de compassion.
20 Zan ɗaura aure da yake cikin aminci za ki kuwa yarda cewa ni ne Ubangiji.
Je t'épouserai en fidélité, et tu connaîtras l'Éternel.
21 “A waccan rana zan amsa,” in ji Ubangiji, “zan amsa wa sararin sama, za su kuwa amsa wa ƙasa;
En ce temps-là je répondrai, dit l'Éternel,
22 ƙasa kuma za tă amsa wa hatsi, sabon ruwan inabi da kuma mai, su kuma za su amsa wa Yezireyel.
Je répondrai aux cieux, et ils répondront à la terre, et la terre répondra au froment, au moût et à l'huile, et ils répondront à Jizréel (que Dieu sème).
23 Zan dasa ta wa kaina a ƙasar; zan shuka ƙaunata ga wanda na ce ‘Ba ƙaunatacciyata ba.’ Zan faɗa wa waɗanda a ce ‘Ba mutanena ba,’ ‘Ku mutanena ne’; za su kuwa ce, ‘Kai ne Allahna.’”
Et je la sèmerai pour moi dans la terre, et je ferai miséricorde à Lo-Ruchama; et je dirai à Lo-Ammi: Tu es mon peuple! et il me dira: “Mon Dieu! “