< Hosiya 11 >

1 “Sa’ad da Isra’ila yake yaro, na ƙaunace shi, daga Masar kuma na kira ɗana.
Quand Israël était enfant, je l'aimai, et dès l'Egypte, j'ai adressé des appels à mon fils.
2 Amma yawan kiran da na yi wa Isra’ila haka nesa da ni da suke ta yi. Suka miƙa hadaya ga Ba’al suka kuma ƙona turare ga siffofi.
On leur a adressé des appels et ils se sont détournés. Ils ont offert des sacrifices aux Baals, et de l'encens aux idoles.
3 Ni ne na koya wa Efraim tafiya ina kama su da hannu; amma ba su gane cewa ni ne na warkar da su ba.
Et moi, j'apprenais à marcher à Ephraïm, je les prenais par les bras, et ils n'ont pas compris que je les soignais.
4 Na bishe su da linzamin alheri da tausayi, da ragamar ƙauna; Na cire karkiya daga wuyansu na kuma rusuna na ciyar da su.
Je les menais avec des cordeaux d'humanité, avec des liens d'amour; j'ai été pour eux comme celui qui aurait soulevé le joug de dessus leurs mâchoires, et je me penchai vers lui et je le fis manger.
5 “Ba za su koma Masar ba Assuriya kuma ba za tă yi mulki a bisansu ba saboda sun ƙi su tuba ba?
Il ne retournera pas au pays d'Egypte, et Assur, lui, sera son roi, parce qu'ils n'ont pas voulu se convertir.
6 Takuba za su yi ta wulgawa a biranensu, za su hallaka sandunan ƙarafan ƙofofinsu su kuma kawo ƙarshen ƙulle-ƙullensu.
L'épée sera brandie dans ses villes; elle brisera les verrous et dévorera, à cause de leurs desseins.
7 Mutanena sun ƙudura su juye daga gare ni. Ko da ma suka yi kira ga Mafi Ɗaukaka, ta ko ƙaƙa ba zai girmama su ba.
Mon peuple est décidé à se séparer de moi; on les appelle en haut, mais aucun d'eux ne lève les yeux.
8 “Yaya zan ba da kai, Efraim? Yaya zan miƙa ka, Isra’ila? Yaya zan yi da kai kamar Adma? Yaya zan yi da kai kamar Zeboyim? Zuciyata ta canja a cikina; dukan tausayina ya huru.
Comment te délaisserais-je, Ephraïm, te livrerais-je, Israël? Comment te laisserais-je devenir comme Adama, te rendrais-je comme Séboïm? Mon cœur se retourne en moi, et toutes ensemble, mes compassions s'émeuvent.
9 Ba zan zartar da fushina mai zafi ba, ba kuwa zan juya in ragargaza Efraim ba. Gama ni Allah ne, ba mutum ba, Mai Tsarki a cikinku. Ba zan zo cikin fushi ba.
Je ne donnerai pas cours à l'ardeur de ma colère, je ne détruirai pas de nouveau Ephraïm. Car je suis Dieu, moi, et non pas homme: au milieu de toi est le Saint, et je ne viendrai pas dans ma fureur.
10 Za su bi Ubangiji; zai yi ruri kamar zaki. Sa’ad da ya yi ruri,’ya’yansa za su zo da rawan jiki daga yamma.
Ils iront après Yahweh; comme un lion, il rugira. Quand il rugira, lui, ses fils accourront tremblants, de l'Occident.
11 Za su zo da rawan jiki kamar tsuntsaye daga Masar, kamar kurciyoyi daga Assuriya. Zan zaunar da su a cikin gidajensu,” in ji Ubangiji.
Ils accourront, tremblants comme un oiseau, de l'Egypte, et comme une colombe, du pays d'Assur; et je les ferai habiter dans leurs maisons, — oracle de Yahweh.
12 Mutanen Efraim sun kewaye ni da ƙarairayi, gidan Isra’ila da ruɗu. Mutanen Yahuda kuma suna yi wa Allah ƙin ji, har ma a kan Mai Tsarkin nan mai aminci.
Ephraïm m'a environné de mensonge, et la maison d'Israël de tromperie; Juda aussi est sans frein vis-à-vis de Dieu, et vis-à-vis du Saint, qui est fidèle.

< Hosiya 11 >