< Hosiya 10 >

1 Isra’ila kuringa ce mai yaɗuwa; ya fitar da’ya’ya wa kansa. Yayinda’ya’yan suka ƙaru, ya gina ƙarin bagadai; da ƙasarsa ta wadata, ya yi wa keɓaɓɓun duwatsu ado.
A luxuriant vine is Israel. He bore fruit lavishly. In proportion to the increase of his fruit he increased altars to idols. In proportion to the beauty of his land he made beautiful the sacred pillars.
2 Zuciyarsu masu ruɗu ne, yanzu kuwa dole su ɗauki laifinsu. Ubangiji zai rushe bagadansu yă kuma hallaka keɓaɓɓun duwatsunsu.
Their heart is false, now they must be punished. God himself will break the necks of their altars, he will destroy their sacred pillars.
3 Sa’an nan za su ce, “Ba mu da sarki domin ba mu girmama Ubangiji ba. Amma ko da ma muna da sarki, me zai yi mana?”
Yes, soon they will be saying, ‘We have no king, for we have not revered the Lord, and a king, what could he do for us anyway?’
4 Sun yi alkawura masu yawa, suka yi rantsuwar ƙarya da kuma yarjejjeniyoyi; saboda haka ƙararraki suka taso kamar ciyayi masu dafi da aka nome a gona.
Speaking words, perjuring themselves, making agreements, and litigation springs up like a poisonous weed in a ploughed field.
5 Mutanen da suke zama a Samariya suna tsoro saboda gunki maraƙin Bet-Awen. Mutanensa za su yi makokinsa, haka ma firistocinsa matsafa, waɗanda suka yi farin ciki a kan darajarsa, don an ɗauke ta daga gare su aka kai ta zaman bauta.
The inhabitants of Samaria will tremble with fear for their calf of Beth-aven. Its people will mourn over it, and so will its priests, who had rejoiced for its glory, now departed from it.
6 Za a ɗauke shi a kai Assuriya kamar gandu wa babban sarki. Efraim zai sha kunya; Isra’ila zai sha kunya saboda gumakan itacensa.
It will be carried off to Assyria as a present to the patron king. Disgrace will Ephraim bear and Israel will be ashamed of its idol.
7 Samariya da sarkinta za su ɓace kamar kumfa a bisa ruwaye.
As for Samaria, her king will disappear, like foam on the face of the waters.
8 Za a hallaka masujadai kan tudu na mugunta zunubin Isra’ila ne. Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma su rufe bagadansu. Sa’an nan za su ce wa duwatsu, “Ku rufe mu!” Ga tuddai kuma, “Ku fāɗo a kanmu!”
And the high places of Aven will be destroyed, the shrines of Israel’s sin, thorns and thistles will grow on their altars, and they will say to the mountains, ‘Cover us,’ and to the hills, ‘Fall upon us.’
9 “Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra’ila, a can kuwa kuka ci gaba. Yaƙi bai cimma masu aikata mugunta a Gibeya ba?
From the time of Gibeah, Israel has sinned. There they took their stand. Will not war overtake them in Gibeah because of the wicked?
10 Sa’ad da na ga dama, zan hukunta su; al’ummai za su taru su yi gāba da su don su daure su saboda zunubansu da suka riɓanya.
When I please, I will punish them. Nations will gather against them to chain them for their double crimes.
11 Efraim horarriyar karsana ce mai son sussuka; saboda haka zan sa karkiya a kyakkyawan wuyanta. Zan bi da Efraim, Dole Yahuda yă yi noma, dole kuma Yaƙub yă ja garman noma.
Ephraim indeed was a trained heifer that loved to thresh grain, and I myself laid a yoke upon his fair neck, I made Ephraim draw and Judah must plough, Jacob must turn the soil for himself.
12 Ku shuka wa kanku adalci, ku girbe’ya’yan jinƙai marar ƙarewa, ku kuma nome ƙasar da ba a nome ba; gama lokaci ne na neman Ubangiji, sai ya zo ya zubo adalci a kanku.
Sow for yourselves righteousness, reap the fruits of love. Break up your fallow ground, for it is time to seek the Lord, so righteousness may come to you.
13 Amma kun shuka mugunta, kuka girbe mugu kuka ci’ya’yan ruɗu. Domin kun dogara da ƙarfinku da kuma a jarumawanku masu yawa,
But you have ploughed wickedness, iniquity have you reaped. You have eaten the fruit of lies. Because you have trusted in your own path, in the multitude of your warriors,
14 hayaniyar yaƙi za tă tashi gāba da mutanenku, saboda a ragargaza kagaranku, kamar yadda Shalman ya ragargaza Bet-Arbel a ranar yaƙi, sa’ad da aka fyaɗa uwaye tare da’ya’yansu da ƙasa.
the alarm of war will sound in your cities and all your fortresses will be ruined, as Shalman laid in ruins Beth-arbel in the day of battle, when mothers were dashed to pieces over their children.
15 Haka zai faru da kai, ya Betel, domin muguntarka ta yi yawa. Sa’ad da wannan rana ta zo, za a hallaka sarkin Isra’ila ƙaƙaf.
Thus will I do to you, Bethel, because of the enormity of your wickedness. When dawn breaks, so will the king of Israel be broken.

< Hosiya 10 >