< Hosiya 1 >

1 Maganar Ubangiji da ta zo wa Hosiya ɗan Beyeri a zamanin mulkin Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, sarakunan Yahuda, da zamanin mulkin Yerobowam ɗan Yowash sarkin Isra’ila.
A word of YHWH that has been to Hosea, son of Beeri, in the days of Uzziah, Jotham, Ahaz, Hezekiah, kings of Judah, and in the days of Jeroboam son of Joash, king of Israel:
2 Sa’ad da Ubangiji ya fara magana ta wurin Hosiya, Ubangiji ya ce masa, “Ka tafi, ka auro wa kanka mazinaciya da’ya’yan da aka haifa ta hanyar rashin aminci, domin ƙasar tana da laifin mummunan zina ta wurin rabuwa da Ubangiji.”
The commencement of YHWH’s speaking by Hosea. And YHWH says to Hosea, “Go, take a woman of whoredoms for yourself, and children of whoredoms, for the land goes utterly whoring from after YHWH.”
3 Saboda haka sai ya auri Gomer’yar Dibilayim, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa namiji.
And he goes and takes Gomer daughter of Diblaim, and she conceives and bears a son to him;
4 Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba shi suna Yezireyel, domin ba da daɗewa ba zan hukunta gidan Yehu saboda kisan da aka yi a Yezireyel, zan kuma kawo ƙarshen mulkin Isra’ila.
and YHWH says to him, “Call his name Jezreel, for yet a little, and I have charged the blood of Jezreel on the house of Jehu, and have caused the kingdom of the house of Israel to cease;
5 A wannan rana zan karye ƙarfin Isra’ila a Kwarin Yezireyel.”
and it has come to pass in that day that I have broken the bow of Israel in the Valley of Jezreel.”
6 Gomer ta sāke ɗauki ciki ta kuma haifi’ya mace. Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba ta suna, Lo-Ruhama, gama ba zan ƙara nuna wa gidan Isra’ila ƙauna ba, har da zan gafarta musu.
And she conceives again, and bears a daughter, and He says to him, “Call her name Lo-Ruhamah [(Not Loved)], for I no longer pity the house of Israel, for I utterly take them away;
7 Duk da haka zan nuna ƙauna ga gidan Yahuda; zan kuma cece su, ba da baka, takobi ko yaƙi ba, ko ta wurin dawakai, ko masu hawan dawakai ba, sai ko ta wurin Ubangiji Allahnsu.”
and I pity the house of Judah, and have saved them by their God YHWH, and do not save them by bow, and by sword, and by battle, by horses, and by horsemen.”
8 Bayan ta yaye Lo-Ruhama, sai Gomer ta sāke haifi wani ɗa namiji.
And she weans Lo-Ruhamah, and conceives, and bears a son;
9 Sai Ubangiji ya ce, “Ka ba shi suna Lo-Ammi, gama ku ba mutanena ba ne, ni kuma ba Allahnku ba ne.
and He says, “Call his name Lo-Ammi [(Not My People)], for you [are] not My people, and I am not for you;
10 “Duk da haka Isra’ilawa za su zama kamar yashi a bakin teku, da ba za a iya aunawa ko a ƙirga ba. A inda aka ce musu, ‘Ku ba mutanena ba ne,’ za a kira su ‘’ya’yan Allah mai rai.’
and the number of the sons of Israel has been as the sand of the sea that is not measured nor numbered, and it has come to pass in the place where it is said to them, You [are] not My people, it is said to them, Sons of the Living God;
11 Mutanen Yahuda da mutanen Isra’ila za su sāke haɗu su zama ɗaya, za su kuma naɗa shugaba guda su kuma fita daga ƙasar, gama ranar za tă zama mai girma wa Yezireyel.
and the sons of Judah and the sons of Israel have been gathered together, and they have appointed one head for themselves, and have gone up from the land, for great [is] the day of Jezreel.”

< Hosiya 1 >