< Habakkuk 3 >
1 Addu’ar annabi Habakkuk. A kan shigiyont.
Detta är Propheten Habacucs bön för de oskyldiga.
2 Ya Ubangiji, na ji irin shaharar da ka yi; na yi al’ajabi game da ayyukanka, ya Ubangiji. Ka maimaita su a kwanakinmu, ka sanar da su a lokacinmu; ka yi jinƙai ko a lokacin da kake fushi.
Herre, jag hafver hört ditt rykte, så att jag förskräcktes. Herre, du gör ditt verk lefvande midt i åren, och låter det kunnigt varda midt i åren. När bedröfvelse på färde är, så tänker du uppå barmhertighet.
3 Allah ya zo daga Teman, Mai Tsarkin nan daga Dutsen Faran. (Sela) Ɗaukakarsa ta rufe sammai yabonsa kuma ya cika duniya.
Gud kom sunnanefter, och den Helge ifrå det berget Paran. (Sela) Af hans lof var himmelen full, och af hans äro var jorden full.
4 Darajarsa ta yi kamar fitowar rana; ƙyalƙyali ya wulga daga hannunsa, inda ikonsa yake a ɓoye.
Hans sken var såsom ett ljus, strimmor gingo af hans händer; der var hans magt hemliga.
5 Annoba ta sha gabansa; cuta kuma tana bin bayansa.
För honom gick pestilentie, och plåga gick ut, ehvart han gick.
6 Ya tsaya, ya kuwa girgiza duniya; ya duba, sai ya sa al’ummai suka yi rawan jiki. Tsofaffin duwatsu sun wargaje daɗaɗɗun tuddai kuma suka rurrushe. Hanyoyinsa dawwammamu ne.
Han stod, och mälte landet; han såg till, och förskingrade Hedningarna, så att verldenes berg förkrossad vordo, och sig bocka måste alle högar i verldene, då han gick uti verldene.
7 Na ga tentin Kushan cikin azaba; wuraren zaman Midiyan cikin damuwa.
Jag såg de Ethiopers hyddor i vedermödo, och de Midianiters tjäll bedröfvad.
8 Ka ji haushin koguna ne, ya Ubangiji? Ko kuwa ka hasala da rafuffuka ne? Ko ka yi fushi da teku ne sa’ad da ka hau dawakanka da kuma kekunan yaƙinka masu nasara?
Vast du icke, Herre, vred i flodene; och din grymhet i vattnom, och din ogunst i hafvena? då du redst på dina hästar, och dine vagnar hehöllo segren.
9 Ka ja bakanka, ka nemi a ba ka kibiyoyi masu yawa. (Sela) Ka raba duniya da koguna;
Du drog fram bågan, såsom du slägterna svorit hade; (Sela) och delade strömmarna i landena.
10 duwatsu sun gan ka sai suka ƙame. Ruwaye masu hauka sun yi ta fantsamawa; zurfafa suka yi ruri suka tā da raƙuman ruwansu sama.
Bergen sågo dig, och vordo bedröfvad; vattuströmmen gick sin kos, djupet lät höra sig, höjden hof sina händer upp.
11 Rana da wata suka tsaya cik a sammai da ganin kibiyoyinka masu wucewa fyu, da ganin hasken māshinka mai walƙiya.
Sol och måne stodo stilla. Dine pilar foro bortåt med ett sken, och din glafven med ljungelds blänkande.
12 Cikin hasala ka ratsa duniya cikin fushi kuma ka tattake ƙasashe.
Du nedertrampade landet i vrede, och söndertröskade Hedningarna i grymhet.
13 Ka fito don ka fanshi mutanenka, don ceci shafaffenka. Ka ragargaza shugaban ƙasar mugaye, ka tuɓe shi daga kai har ƙafa. (Sela)
Du drog ut till att hjelpa dino folke, till att hjelpa dinom smorda; du sönderslogst hufvudet uti dens ogudaktigas huse, och blottade grunden allt intill halsen; (Sela)
14 Da māshinsa ka soki kansa sa’ad da jarumawansa suka fito don su tarwatse mu, suna farin ciki sai ka ce masu shirin cinye matalautan da suke a ɓoye.
O! att du ville banna hufvudens spiror, samt med dess byar, hvilke, såsom ett väder, komma till att förströ mig, och glädja sig, lika som de uppslukte de elända hemliga.
15 Ka tattake teku da dawakanka, kana kaɗa manyan ruwaye.
Dine hästar gå i hafvena, uti stor vattens träck.
16 Na ji sai zuciyata ta buga, leɓunana sun yi rawa da jin murya; ƙasusuwana suka ruɓe, ƙafafuna kuma sun yi rawa. Duk da haka zan jira da haƙuri ga ranar bala’i ta zo a kan al’umman nan mai kawo mana hari.
Efter jag sådant hörer, så är min buk bedröfvad; mine läppar darra af rop var går i minom ben om; jag är bedröfvad vid mig. Ack! att jag hvila måtte i bedröfvelsens tid, då vi uppdrage till det folk, som emot oss strider.
17 Ko da yake itace ɓaure bai tohu ba, ba kuma’ya’ya a kuringar inabi, ko da yake zaitun bai ba da amfani ba, gonaki kuma ba su ba da abinci ba, ko da yake babu tumaki a garke, ba kuma shanu a turaku,
Ty fikonaträt skall icke grönskas, och der skall ingen frukt vara på vinträn; arbetet uppå oljoträt felar, och åkrarna bära ingen födo; och fåren skola ryckas utu fårahusen, och intet fä skall vara uti fähusen.
18 duk da haka zan yi farin ciki da Ubangiji, zan yi murna da Allah Mai Cetona.
Men jag vill glädja mig af Herranom, och glad vara i Gudi, minom Frälsare.
19 Ubangiji Mai Iko Duka shi ne ƙarfina; yakan mai da ƙafafuna kamar na barewa, yakan sa in yi tafiya a wurare masu tsayi. Domin mai bi da kaɗe-kaɗe. A kan kayan kiɗi masu tsirkiyata.
Ty Herren Herren är min kraft, och han skall göra mina fötter lika som hjortafötter; och skall föra mig upp i höjdena, så att jag sjunger på min strängaspel.