< Habakkuk 3 >

1 Addu’ar annabi Habakkuk. A kan shigiyont.
Seigneur, j'ai entendu Ta voix, et j'ai eu crainte.
2 Ya Ubangiji, na ji irin shaharar da ka yi; na yi al’ajabi game da ayyukanka, ya Ubangiji. Ka maimaita su a kwanakinmu, ka sanar da su a lokacinmu; ka yi jinƙai ko a lokacin da kake fushi.
J'ai considéré Tes œuvres, et je me suis extasié. Entre deux animaux Tu Te manifestes; quand les années seront proches, on Te connaîtra; quand les temps seront venus, Tu apparaîtras; quand mon âme est troublée de Ta colère, souviens-Toi de Ta miséricorde.
3 Allah ya zo daga Teman, Mai Tsarkin nan daga Dutsen Faran. (Sela) Ɗaukakarsa ta rufe sammai yabonsa kuma ya cika duniya.
Dieu viendra de Théman, et le Saint de la montagne ténébreuse de Pharan. Sa vertu est le vêtement des cieux, et la terre est pleine de Sa louange.
4 Darajarsa ta yi kamar fitowar rana; ƙyalƙyali ya wulga daga hannunsa, inda ikonsa yake a ɓoye.
Sa splendeur sera comme la lumière; Il a dans Sa main des cornes (de puissance), et de la force Il a fait un puissant amour.
5 Annoba ta sha gabansa; cuta kuma tana bin bayansa.
Devant Sa face ira une parole; elle cheminera dans les plaines; sur Ses pieds
6 Ya tsaya, ya kuwa girgiza duniya; ya duba, sai ya sa al’ummai suka yi rawan jiki. Tsofaffin duwatsu sun wargaje daɗaɗɗun tuddai kuma suka rurrushe. Hanyoyinsa dawwammamu ne.
Il S'est dressé, et la terre en a tremblé; Il a regardé, et les nations se sont évanouies. les montagnes ont été violemment agitées; les collines se sont fendues, sous les pas de Sa marche éternelle.
7 Na ga tentin Kushan cikin azaba; wuraren zaman Midiyan cikin damuwa.
À cause des troubles, j'ai vu les tentes des Éthiopiens renversées; les tentes de la terre de Madian seront aussi frappées d'épouvante.
8 Ka ji haushin koguna ne, ya Ubangiji? Ko kuwa ka hasala da rafuffuka ne? Ko ka yi fushi da teku ne sa’ad da ka hau dawakanka da kuma kekunan yaƙinka masu nasara?
Seigneur, est-ce contre les fleuves que Tu es irrité? Est-ce que Ta colère s'en prend aux fleuves? Attaques-Tu la mer? Car Tu es monté sur Ton char, et Tes chevaux amènent le salut.
9 Ka ja bakanka, ka nemi a ba ka kibiyoyi masu yawa. (Sela) Ka raba duniya da koguna;
Tu as fortement tendu ton arc contre les sceptres, dit le Seigneur. le cours des fleuves sera déchiré.
10 duwatsu sun gan ka sai suka ƙame. Ruwaye masu hauka sun yi ta fantsamawa; zurfafa suka yi ruri suka tā da raƙuman ruwansu sama.
Les peuples Te verront, Seigneur, et ils auront des douleurs comme celles de l'enfantement. Quand Tu détruis la voie par une inondation, l'abîme a fait entendre sa voix, et il a élevé ses vagues contre Toi.
11 Rana da wata suka tsaya cik a sammai da ganin kibiyoyinka masu wucewa fyu, da ganin hasken māshinka mai walƙiya.
Le soleil s'est levé; la lune s'est tenue au lieu qui lui est prescrit: Tes rayons s'avanceront dans la lumière, à la lueur des éclairs qui jaillissent de Tes armes.
12 Cikin hasala ka ratsa duniya cikin fushi kuma ka tattake ƙasashe.
Par Tes menaces, Tu abaisses la terre, et dans Ton courroux Tu abats les nations.
13 Ka fito don ka fanshi mutanenka, don ceci shafaffenka. Ka ragargaza shugaban ƙasar mugaye, ka tuɓe shi daga kai har ƙafa. (Sela)
Tu es venu pour le salut de Ton peuple, pour sauver Ton Christ; Tu enverras la mort sur la tête des impies; Tu les as chargés de chaînes jusqu'au cou.
14 Da māshinsa ka soki kansa sa’ad da jarumawansa suka fito don su tarwatse mu, suna farin ciki sai ka ce masu shirin cinye matalautan da suke a ɓoye.
Tu as frappé de stupeur les bêtes des puissants; ils en trembleront; ils laisseront voir leur frein en ouvrant la bouche, comme un pauvre qui mange en se cachant.
15 Ka tattake teku da dawakanka, kana kaɗa manyan ruwaye.
Et, monté sur Tes chevaux, Tu es entré dans la mer, et ils en ont troublé l'eau profonde.
16 Na ji sai zuciyata ta buga, leɓunana sun yi rawa da jin murya; ƙasusuwana suka ruɓe, ƙafafuna kuma sun yi rawa. Duk da haka zan jira da haƙuri ga ranar bala’i ta zo a kan al’umman nan mai kawo mana hari.
J'ai veillé, et mes entrailles ont frémi au son de la prière de mes lèvres, et l'effroi est entré dans mes os, et tout mon être a été bouleversé. Je me reposerai au jour de l'affliction, et je monterai chez le peuple où je suis passager.
17 Ko da yake itace ɓaure bai tohu ba, ba kuma’ya’ya a kuringar inabi, ko da yake zaitun bai ba da amfani ba, gonaki kuma ba su ba da abinci ba, ko da yake babu tumaki a garke, ba kuma shanu a turaku,
Car alors le figuier ne portera pas de fruits; il n'y aura pas de raisin à la vigne; l'œuvre de l'olivier sera trompeuse, et les champs ne produiront pas de nourriture. Les brebis manqueront de fourrage, et il n'y aura pas de bœufs à la crèche.
18 duk da haka zan yi farin ciki da Ubangiji, zan yi murna da Allah Mai Cetona.
Pour moi, je tressaillirai dans le Seigneur; je mettrai ma joie en Dieu, mon Sauveur.
19 Ubangiji Mai Iko Duka shi ne ƙarfina; yakan mai da ƙafafuna kamar na barewa, yakan sa in yi tafiya a wurare masu tsayi. Domin mai bi da kaɗe-kaɗe. A kan kayan kiɗi masu tsirkiyata.
Le Seigneur mon Dieu est ma force; Il placera mes pieds sur une base inébranlable; Il m'a fait monter sur les hautes cimes, pour chanter en Son honneur un chant de triomphe.

< Habakkuk 3 >