< Habakkuk 3 >
1 Addu’ar annabi Habakkuk. A kan shigiyont.
A prayer of Habakkuk the prophet on Shigionoth.
2 Ya Ubangiji, na ji irin shaharar da ka yi; na yi al’ajabi game da ayyukanka, ya Ubangiji. Ka maimaita su a kwanakinmu, ka sanar da su a lokacinmu; ka yi jinƙai ko a lokacin da kake fushi.
O LORD, I have heard your speech, and was afraid: O LORD, revive your work in the middle of the years, in the middle of the years make known; in wrath remember mercy.
3 Allah ya zo daga Teman, Mai Tsarkin nan daga Dutsen Faran. (Sela) Ɗaukakarsa ta rufe sammai yabonsa kuma ya cika duniya.
God came from Teman, and the Holy One from mount Paran. (Selah) His glory covered the heavens, and the earth was full of his praise.
4 Darajarsa ta yi kamar fitowar rana; ƙyalƙyali ya wulga daga hannunsa, inda ikonsa yake a ɓoye.
And his brightness was as the light; he had horns coming out of his hand: and there was the hiding of his power.
5 Annoba ta sha gabansa; cuta kuma tana bin bayansa.
Before him went the pestilence, and burning coals went forth at his feet.
6 Ya tsaya, ya kuwa girgiza duniya; ya duba, sai ya sa al’ummai suka yi rawan jiki. Tsofaffin duwatsu sun wargaje daɗaɗɗun tuddai kuma suka rurrushe. Hanyoyinsa dawwammamu ne.
He stood, and measured the earth: he beheld, and drove asunder the nations; and the everlasting mountains were scattered, the perpetual hills did bow: his ways are everlasting.
7 Na ga tentin Kushan cikin azaba; wuraren zaman Midiyan cikin damuwa.
I saw the tents of Cushan in affliction: and the curtains of the land of Midian did tremble.
8 Ka ji haushin koguna ne, ya Ubangiji? Ko kuwa ka hasala da rafuffuka ne? Ko ka yi fushi da teku ne sa’ad da ka hau dawakanka da kuma kekunan yaƙinka masu nasara?
Was the LORD displeased against the rivers? was your anger against the rivers? was your wrath against the sea, that you did ride on your horses and your chariots of salvation?
9 Ka ja bakanka, ka nemi a ba ka kibiyoyi masu yawa. (Sela) Ka raba duniya da koguna;
Your bow was made quite naked, according to the oaths of the tribes, even your word. (Selah) You did split the earth with rivers.
10 duwatsu sun gan ka sai suka ƙame. Ruwaye masu hauka sun yi ta fantsamawa; zurfafa suka yi ruri suka tā da raƙuman ruwansu sama.
The mountains saw you, and they trembled: the overflowing of the water passed by: the deep uttered his voice, and lifted up his hands on high.
11 Rana da wata suka tsaya cik a sammai da ganin kibiyoyinka masu wucewa fyu, da ganin hasken māshinka mai walƙiya.
The sun and moon stood still in their habitation: at the light of your arrows they went, and at the shining of your glittering spear.
12 Cikin hasala ka ratsa duniya cikin fushi kuma ka tattake ƙasashe.
You did march through the land in indignation, you did thresh the heathen in anger.
13 Ka fito don ka fanshi mutanenka, don ceci shafaffenka. Ka ragargaza shugaban ƙasar mugaye, ka tuɓe shi daga kai har ƙafa. (Sela)
You went forth for the salvation of your people, even for salvation with your anointed; you wounded the head out of the house of the wicked, by discovering the foundation to the neck. (Selah)
14 Da māshinsa ka soki kansa sa’ad da jarumawansa suka fito don su tarwatse mu, suna farin ciki sai ka ce masu shirin cinye matalautan da suke a ɓoye.
You did strike through with his staves the head of his villages: they came out as a whirlwind to scatter me: their rejoicing was as to devour the poor secretly.
15 Ka tattake teku da dawakanka, kana kaɗa manyan ruwaye.
You did walk through the sea with your horses, through the heap of great waters.
16 Na ji sai zuciyata ta buga, leɓunana sun yi rawa da jin murya; ƙasusuwana suka ruɓe, ƙafafuna kuma sun yi rawa. Duk da haka zan jira da haƙuri ga ranar bala’i ta zo a kan al’umman nan mai kawo mana hari.
When I heard, my belly trembled; my lips quivered at the voice: rottenness entered into my bones, and I trembled in myself, that I might rest in the day of trouble: when he comes up to the people, he will invade them with his troops.
17 Ko da yake itace ɓaure bai tohu ba, ba kuma’ya’ya a kuringar inabi, ko da yake zaitun bai ba da amfani ba, gonaki kuma ba su ba da abinci ba, ko da yake babu tumaki a garke, ba kuma shanu a turaku,
Although the fig tree shall not blossom, neither shall fruit be in the vines; the labor of the olive shall fail, and the fields shall yield no meat; the flock shall be cut off from the fold, and there shall be no herd in the stalls:
18 duk da haka zan yi farin ciki da Ubangiji, zan yi murna da Allah Mai Cetona.
Yet I will rejoice in the LORD, I will joy in the God of my salvation.
19 Ubangiji Mai Iko Duka shi ne ƙarfina; yakan mai da ƙafafuna kamar na barewa, yakan sa in yi tafiya a wurare masu tsayi. Domin mai bi da kaɗe-kaɗe. A kan kayan kiɗi masu tsirkiyata.
The LORD God is my strength, and he will make my feet like hinds’ feet, and he will make me to walk on my high places. To the chief singer on my stringed instruments.