+ Farawa 1 >

1 A farko-farko, Allah ya halicci sama da ƙasa.
Al principio Dios hizo el cielo y la tierra.
2 To, ƙasa dai ba ta da siffa, babu kuma kome a cikinta, duhu ne kawai ya rufe ko’ina, Ruhun Allah kuwa yana yawo a kan ruwan.
Y la tierra estaba desordenada y sin forma; y estaba oscuro sobre la faz del abismo: y el Espíritu de Dios se movía sobre la faz de las aguas.
3 Sai Allah ya ce, “Bari haske yă kasance,” sai kuwa ga haske.
Y dijo Dios: Hágase la luz, y fué la luz.
4 Allah ya ga hasken yana da kyau, sai ya raba tsakanin hasken da duhu.
Y mirando Dios a la luz, vio que era buena; y Dios hizo una división entre la luz y la oscuridad,
5 Allah ya kira hasken “yini,” ya kuma kira duhun “dare.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta fari ke nan.
Nombrando la luz, el día y la oscuridad, la noche. Y hubo tarde y hubo mañana, el primer día.
6 Allah ya ce, “Bari sarari yă kasance tsakanin ruwaye domin yă raba ruwa da ruwa.”
Y dijo Dios: Haya un arco visible del cielo que se extiende sobre las aguas, separando las aguas de las aguas.
7 Saboda haka Allah ya yi sarari ya raba ruwan da yake ƙarƙashin sararin da ruwan da yake bisansa. Haka kuwa ya kasance.
E hizo la tierra, Dios él Señor el arco visible del cielo para dividir entre las aguas que estaban debajo del arco y las que estaban sobre él; y fue así.
8 Allah ya kira sararin “sama.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyu ke nan.
Y Dios le dio al arco el nombre de Cielo. Y hubo tarde y hubo mañana, el segundo día.
9 Allah ya ce, “Bari ruwan da yake ƙarƙashin sama yă tattaru wuri ɗaya, bari kuma busasshiyar ƙasa tă bayyana.” Haka kuwa ya kasance.
Y dijo Dios: Júntense las aguas debajo de los cielos en un lugar, y que se vea la tierra seca; y fue así.
10 Allah ya kira busasshiyar ƙasar “doron ƙasa,” ruwan da ya taru kuma, ya kira “tekuna.” Allah ya ga yana da kyau.
Y Dios dio a la tierra firme el nombre de la tierra; y las aguas juntas en su lugar fueron llamadas mares; y Dios vio que era bueno.
11 Sa’an nan Allah ya ce, “Bari ƙasa tă fid da tsire-tsire, da shuke-shuke, da itatuwa a bisa ƙasa masu ba da amfani da’ya’ya a cikinsu, bisa ga irinsu.” Haka kuwa ya kasance.
Y dijo Dios: que produzca hierba en la tierra, y plantas que produzcan semilla, y árboles frutales que dan fruto, en lo cual está su simiente, según su género; y fue así.
12 Ƙasar ta fid da tsire-tsire, da shuke-shuke masu ba da’ya’ya bisa ga irinsu, ta fid kuma da itatuwa masu ba da’ya’ya da iri a cikinsu bisa ga irinsu. Allah ya ga yana da kyau.
Y produjo hierba sobre la tierra, y toda planta que produce simiente de su género, y todo árbol que produce fruto, en el cual está su simiente, de su especie; y vio Dios que era bueno.
13 Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta uku ke nan.
Y fue la tarde y la mañana, el tercer día.
14 Allah kuma ya ce, “Bari haskoki su kasance a sararin sama domin su raba yini da dare, bari su zama alamu domin su nuna yanayi, da ranaku, da kuma shekaru,
Y dijo Dios: Haya luces en el arco del cielo, para división entre el día y la noche, y sean por señales, y para marcar los cambios del año, y por días y años;
15 bari kuma haskokin su kasance a sararin sama domin su ba da haske a duniya.” Haka kuwa ya kasance.
Y sean por lumbreras en el arco del cielo para alumbrar la tierra; y fue así.
16 Allah ya yi manyan haskoki biyu, babban hasken yă mallaki yini, ƙaramin kuma yă mallaki dare. Ya kuma yi taurari.
E hizo Dios él Señor las dos grandes lámparas: la lumbrera mayor para ser la gobernante del día, y la lumbrera menor para ser el soberano de la noche; e hizo las estrellas.
17 Allah ya sa su a sararin sama domin su ba da haske a duniya,
Y los puso Dios en el arco del cielo, para alumbrar la tierra;
18 su mallaki yini da kuma dare, su kuma raba haske da duhu. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
para tener dominio sobre el día y la noche, y para una división entre la luz y la oscuridad: y Dios vio que era bueno.
19 Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta huɗu ke nan.
Y fue la tarde y la mañana, el cuarto día.
20 Allah ya ce, “Bari ruwa yă cika da halittu masu rai, bari tsuntsaye kuma su tashi sama a bisa duniya a sararin sama.”
Y dijo Dios: Las aguas produzcan seres vivientes, y las aves vuelen sobre la tierra debajo del arco del cielo.
21 Allah ya halicci manyan halittun teku, da kowane mai rai da abin da yake motsi a ruwa, bisa ga irinsu, da kuma kowane tsuntsu mai fiffike bisa ga irinsa. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
E hizo Dios grandes bestias de mar, y todo tipo de cosas vivas que las aguas producen, con las cuales se llenaron las aguas, y todo tipo de ave alada; y vio Dios que era bueno.
22 Allah ya albarkace su ya ce, “Ku yi ta haihuwa ku kuma ƙaru da yawa, ku cika ruwan tekuna, bari kuma tsuntsaye su yi yawa a bisa duniya.”
Y Dios les bendijo, diciendo: Sé fértil y multiplícate, llenando todas las aguas de los mares, y que las aves crezcan en la tierra.
23 Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyar ke nan.
Y fue la tarde y la mañana, el quinto día.
24 Allah kuwa ya ce, “Bari ƙasa tă ba da halittu masu rai bisa ga irinsu; dabbobi da halittu masu rarrafe, da kuma namun jeji, kowane bisa ga irinsa.” Haka kuwa ya kasance.
Y dijo Dios: La tierra dé a luz toda clase de seres vivientes, vacas y todo lo que se mueve sobre la tierra, y las bestias de la tierra según su género; y fue así.
25 Allah ya halicci namun jeji bisa ga irinsu, dabbobi bisa ga irinsu, da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa bisa ga irinsu. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
Y Dios hizo las bestias de la tierra según su género, y el ganado según su género, y todo lo que se movía sobre la faz de la tierra según su género; y vio Dios que era bueno.
26 Sa’an nan Allah ya ce, “Bari mu yi mutum cikin siffarmu, cikin kamanninmu, bari kuma su yi mulki a bisa kifin teku, tsuntsayen sama, da kuma dabbobi, su yi mulki a bisa dukan duniya, da kuma a bisa dukan halittu, da masu rarrafe a ƙasa.”
Y dijo Dios: Hagamos al hombre a nuestra imagen, como nosotros; y gobierne sobre los peces del mar, y sobre las aves del cielo, y sobre el ganado, y sobre toda la tierra, y sobre todo ser viviente. cosa que se arrastra en la tierra.
27 Saboda haka Allah ya halicci mutum cikin siffarsa. Cikin kamannin Allah, Allah ya halicci mutum. Miji da mace ya halicce su.
E hizo Dios al hombre a su imagen, a imagen de Dios lo hizo; varón y hembra los hizo.
28 Allah ya albarkace su, ya kuma ce musu, “Ku yi ta haihuwa ku ƙaru da yawa, ku mamaye duniya, ku mallake ta. Ku yi mulki a bisa kifin teku, da tsuntsayen sararin sama, da kuma bisa kowace halitta mai rai wadda take rarrafe a ƙasa.”
Y Dios los bendijo, y les dijo: Sean fértiles y tengan más, y hagan que la tierra esté llena y sean dueños de ella; sean los gobernantes sobre los peces del mar y sobre las aves del aire y sobre todos los seres vivos que se mueven en la tierra.
29 Sa’an nan Allah ya ce, “Ga shi, na ba ku kowane tsiro mai ba da’ya’ya masu kwaya da suke a fāɗin duniya, da dukan itatuwa masu ba da’ya’ya, don su zama abinci a gare ku.
Y dijo Dios: Mira, yo te he dado toda planta que produce simiente sobre la faz de toda la tierra, y todo árbol que tiene fruto que da semilla; para tu alimento será;
30 Na kuma ba da dukan dabbobin ƙasa, da dukan tsuntsayen sama, da dukan abin da yake rarrafe a ƙasa, da dai iyakar abin da yake numfashi; haka kuma na ba da ganyaye su zama abinci.” Haka kuwa ya kasance.
Y a toda bestia de la tierra, y a toda ave del cielo, y a todo ser viviente que se mueve sobre la faz de la tierra, he dado toda planta verde para alimento; y fue así.
31 Allah ya ga dukan abin da ya yi, yana da kyau ƙwarai. Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta shida ke nan.
Y vio Dios todo lo que había hecho, y fue muy bueno. Y hubo tarde y hubo mañana, el sexto día.

+ Farawa 1 >