+ Farawa 1 >

1 A farko-farko, Allah ya halicci sama da ƙasa.
I KINOHI hana ke Akua i ka lani a me ka honua.
2 To, ƙasa dai ba ta da siffa, babu kuma kome a cikinta, duhu ne kawai ya rufe ko’ina, Ruhun Allah kuwa yana yawo a kan ruwan.
He ano ole ka honua, ua olohelohe; a maluna no o ka hohonu ka pouli. Hoopunana iho la ka Uhane o ke Akua maluna o ka wai.
3 Sai Allah ya ce, “Bari haske yă kasance,” sai kuwa ga haske.
I iho la ke Akua, I malamalama; a ua malamalama ae la.
4 Allah ya ga hasken yana da kyau, sai ya raba tsakanin hasken da duhu.
Nana ae la ke Akua i ka malamalama, ua maikai: a hookaawale ae la ke Akua mawaena o ka malamalama, a me ka pouli.
5 Allah ya kira hasken “yini,” ya kuma kira duhun “dare.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta fari ke nan.
Kapa mai la ke Akua i ka malamalama, he Ao, a kapa mai hoi ia i ka pouli, he Po. A o ke ahiahi a me ke kakahiaka, o ka la mua ia.
6 Allah ya ce, “Bari sarari yă kasance tsakanin ruwaye domin yă raba ruwa da ruwa.”
I iho la ke Akua, I aouli mawaena o na wai, i mea hookaawale i kekahi wai me kekahi wai.
7 Saboda haka Allah ya yi sarari ya raba ruwan da yake ƙarƙashin sararin da ruwan da yake bisansa. Haka kuwa ya kasance.
Hana iho la ke Akua i ke aouli; a hookaawale ae la ia i ka wai malalo o ke aouli, me ka wai maluna o ke aouli: a pela io no.
8 Allah ya kira sararin “sama.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyu ke nan.
Kapa iho la ke Akua i ke aouli, he Lani. A o ke ahiahi a me ke kakahiaka, o ka lua ia o ka la.
9 Allah ya ce, “Bari ruwan da yake ƙarƙashin sama yă tattaru wuri ɗaya, bari kuma busasshiyar ƙasa tă bayyana.” Haka kuwa ya kasance.
I iho la ke Akua, E hui pu na wai malalo o ka lani i kahi hookahi, i ikea ai kahi maloo: a pela io no.
10 Allah ya kira busasshiyar ƙasar “doron ƙasa,” ruwan da ya taru kuma, ya kira “tekuna.” Allah ya ga yana da kyau.
Kapa iho la ke Akua i kahi maloo, he Aina; a kapa iho la oia i na wai i hui pu ia 'i, o na moana: a nana ae la ke Akua, ua maikai.
11 Sa’an nan Allah ya ce, “Bari ƙasa tă fid da tsire-tsire, da shuke-shuke, da itatuwa a bisa ƙasa masu ba da amfani da’ya’ya a cikinsu, bisa ga irinsu.” Haka kuwa ya kasance.
I iho la ke Akua, E hooulu mai ka honua i ka mauu, a me ka launahele e hua ana i ka hua, a me ka laau hua e hua ana hoi ma kona ano iho, iloko ona iho kona hua maluna o ka honua: a pela io no.
12 Ƙasar ta fid da tsire-tsire, da shuke-shuke masu ba da’ya’ya bisa ga irinsu, ta fid kuma da itatuwa masu ba da’ya’ya da iri a cikinsu bisa ga irinsu. Allah ya ga yana da kyau.
A hooulu mai la ka honua i ka mauu, a me ka launahele e hua ana i ka hua ma kona ano iho, a me ka laau e hua ana i ka hua, iloko ona kona hua ma kona ano iho: nana iho la hoi ke Akua, ua maikai.
13 Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta uku ke nan.
A o ke ahiahi a me ke kakahiaka, o ke kolu ia o ka la.
14 Allah kuma ya ce, “Bari haskoki su kasance a sararin sama domin su raba yini da dare, bari su zama alamu domin su nuna yanayi, da ranaku, da kuma shekaru,
I iho la ke Akua, I mau malamalama iloko o ke aouli o ka lani, i mea hookaawale i ke ao a me ka po; i mau hoailona lakou no na kau, a no na la, a me na makahiki:
15 bari kuma haskokin su kasance a sararin sama domin su ba da haske a duniya.” Haka kuwa ya kasance.
I mau kukui hoi lakou iloko o ke aouli o ka lani, e hoomalamalama mai ai i ka honua: a pela io no.
16 Allah ya yi manyan haskoki biyu, babban hasken yă mallaki yini, ƙaramin kuma yă mallaki dare. Ya kuma yi taurari.
Hana iho la ke Akua i na malamalama nui elua: o ka malamalama nui, e alii ai maluna o ke ao, a o ka malamalama uuku iho, e alii ai maluna o ka po, a me na hoku hoi.
17 Allah ya sa su a sararin sama domin su ba da haske a duniya,
Kau aku la ke Akua ia mau mea ma ke aouli o ka lani, e hoomalamalama mai ai i ka honua,
18 su mallaki yini da kuma dare, su kuma raba haske da duhu. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
E hooalii hoi maluna o ke ao a me ka po, a e hookaawale ae i ka malamalama a me ka pouli: a nana iho la ke Akua, ua maikai.
19 Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta huɗu ke nan.
A o ke ahiahi a me ke kakahiaka, o ka ha ia o ka la.
20 Allah ya ce, “Bari ruwa yă cika da halittu masu rai, bari tsuntsaye kuma su tashi sama a bisa duniya a sararin sama.”
I iho la ke Akua, E hoohua nui mai na wai i na mea ola e holo ana, a me na manu e lele ae maluna o ka honua, ma ka lewa akea o ka lani.
21 Allah ya halicci manyan halittun teku, da kowane mai rai da abin da yake motsi a ruwa, bisa ga irinsu, da kuma kowane tsuntsu mai fiffike bisa ga irinsa. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
Hana iho la ke Akua i na ia nui, a me na mea ola a pau e holo ana, a ka wai i hoohua nui mai ai ma ko lakou ano iho a me na mea eheu hoi a pau ma ko lakou ano iho: a nana iho la ke Akua, ua maikai.
22 Allah ya albarkace su ya ce, “Ku yi ta haihuwa ku kuma ƙaru da yawa, ku cika ruwan tekuna, bari kuma tsuntsaye su yi yawa a bisa duniya.”
Hoomaikai iho la ke Akua ia mau mea, i iho la, E hoohua ae oukou e hoolaha nui hoi, a e hoopiha i na wai o na moana; a e hoolaha ae na manu maluna o ka honua.
23 Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyar ke nan.
O ke kakahiaka a me ke ahiahi, o ka lima ia o ka la.
24 Allah kuwa ya ce, “Bari ƙasa tă ba da halittu masu rai bisa ga irinsu; dabbobi da halittu masu rarrafe, da kuma namun jeji, kowane bisa ga irinsa.” Haka kuwa ya kasance.
I iho la ke Akua, E hoohua mai ka honua i ka mea ola ma kona ano iho, i ka holoholona laka, me ka mea kolo, a me ka holoholona hihiu ma kona ano iho: a pela io no.
25 Allah ya halicci namun jeji bisa ga irinsu, dabbobi bisa ga irinsu, da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa bisa ga irinsu. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
Hana iho la ke Akua i ka holoholona hihiu ma kona ano iho, me na holoholona laka ma ko lakou ano iho, a me na mea kolo a pau o ka honua ma ko lakou ano iho: a nana iho la ke Akua, ua maikai.
26 Sa’an nan Allah ya ce, “Bari mu yi mutum cikin siffarmu, cikin kamanninmu, bari kuma su yi mulki a bisa kifin teku, tsuntsayen sama, da kuma dabbobi, su yi mulki a bisa dukan duniya, da kuma a bisa dukan halittu, da masu rarrafe a ƙasa.”
I iho la ke Akua, E hana kakou i ke kanaka o ku ia kakou, ma ka like ana me kakou iho: a e hooalii ia ia maluna o na ia o ke kai, maluna hoi o na manu o ka lewa, maluna hoi o na holoholona laka, a maluna hoi o ka honua a pau, a maluna no hoi o na mea kolo a pau e kolo ana ma ka honua.
27 Saboda haka Allah ya halicci mutum cikin siffarsa. Cikin kamannin Allah, Allah ya halicci mutum. Miji da mace ya halicce su.
Hana iho la ke Akua i ke kanaka ma kona ano iho, ma ke ano o ke Akua oia i hana'i ia ia; hana mai la ia i kane a i wahine.
28 Allah ya albarkace su, ya kuma ce musu, “Ku yi ta haihuwa ku ƙaru da yawa, ku mamaye duniya, ku mallake ta. Ku yi mulki a bisa kifin teku, da tsuntsayen sararin sama, da kuma bisa kowace halitta mai rai wadda take rarrafe a ƙasa.”
Hoomaikai mai la ke Akua ia laua, i mai la hoi ke Akua ia laua, E hoohua ae olua, e hoolaha hoi, e hoopiha i ka honua, a e lanakila maluna, a e noho alii maluna o na ia o ke kai, a me na manu o ka lewa, a me na mea a pau e kolo ana maluna o ka honua.
29 Sa’an nan Allah ya ce, “Ga shi, na ba ku kowane tsiro mai ba da’ya’ya masu kwaya da suke a fāɗin duniya, da dukan itatuwa masu ba da’ya’ya, don su zama abinci a gare ku.
I mai la ke Akua, Aia hoi, na haawi aku au na olua i na launahele a pau e hua ana i ka hua maluna o ka honua a pau, a me na laau a pau iloko ona ka hua o ka laau e hua ana i ka hua; he mea ai ia na olua.
30 Na kuma ba da dukan dabbobin ƙasa, da dukan tsuntsayen sama, da dukan abin da yake rarrafe a ƙasa, da dai iyakar abin da yake numfashi; haka kuma na ba da ganyaye su zama abinci.” Haka kuwa ya kasance.
A na ka poe holoholona a pau o ka honua, me na manu a pau o ka lewa, a me na mea a pau e kolo ana ma ka honua, na mea e ola ana, na lakou ka nahelehele a pau i mea ai: a pela io no.
31 Allah ya ga dukan abin da ya yi, yana da kyau ƙwarai. Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta shida ke nan.
Nana iho la ke Akua i na mea a pau ana i hana'i, aia hoi, ua maikai wale no. A o ke ahiahi a me ke kakahiaka, o ke ono ia o ka la.

+ Farawa 1 >