< Farawa 8 >

1 Amma Allah ya tuna da Nuhu da dukan namun jeji da dabbobin da suke tare da shi a cikin jirgi, ya kuma aika da wata iska ta hura dukan duniya, ruwan kuwa ya janye.
But God (did not forget/thought) about Noah and all the wild animals and all the kinds of livestock that were with him in the boat. So one day God sent a wind to blow across the earth, and the wind caused the water [to begin] to recede.
2 Aka toshe maɓuɓɓugan zurfafa da ƙofofin ambaliyar sammai, ruwan sama kuma ya daina saukowa daga sarari.
God caused the water that was under the earth to stop bursting forth, and he caused the floodgates of water from the sky to close so that it stopped raining.
3 Ruwan ya janye a hankali daga ƙasa. A ƙarshen kwanaki ɗari da hamsin ɗin, ruwan ya ragu.
The water on the earth gradually receded. 150 days after the flood began,
4 A rana ta goma sha bakwai ga watan bakwai, jirgin ya sauka a duwatsun Ararat.
(on the 17th day of the seventh month [of that year/late in March]), the boat came to rest on one of the mountains in the Ararat region.
5 Ruwan ya ci gaba da janyewa har watan goma. A rana ta fari ga watan goma kuwa ƙwanƙolin duwatsun suka bayyana.
The water continued to recede until, on the first day of the tenth month [of that year], the tops of other mountains became visible.
6 Bayan kwana arba’in, sai Nuhu ya buɗe tagar jirgin da ya yi,
40 days later, Noah opened the window that he had made in the side of the boat, and sent out a raven.
7 ya saki hankaka. Hankaka ya yi ta kai da kawowa har sai da ruwa ya shanye a duniya.
The raven flew back and forth [to and from the boat] until the water was completely gone.
8 Sai ya saki kurciya don yă ga in ruwan ya janye daga doron ƙasa.
Then Noah sent out a dove to find out if the water had all receded on the ground.
9 Amma kurciyar ba tă sami inda za tă sa ƙafafunta ba gama akwai ruwa a dukan doron ƙasa, saboda haka ta komo wurin Nuhu a jirgi. Ya miƙa hannunsa ya ɗauko kurciyar ya shigar da ita wurinsa a cikin jirgi.
But the dove did not find any place to perch, so it flew back to Noah in the boat, because there was still water all over the surface of the earth. So Noah reached out his hand and took the dove back inside the boat.
10 Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar daga jirgi.
Noah waited seven more days. Then he sent the dove out of the boat again.
11 Sa’ad da kurciya ta komo wurinsa da yamma, sai ga ɗanyen ganyen zaitun da ta tsinko a bakinta! Sa’an nan Nuhu ya san cewa ruwa ya janye daga duniya.
This time the dove returned to him in the evening and, [surprisingly], in its beak there was a leaf from an olive tree that the dove had just plucked. Then Noah knew that the water had truly receded from the surface of the ground.
12 Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar, amma a wannan ƙaro ba tă komo wurinsa ba.
Noah waited seven more days. Then he sent the dove out again, but this time it did not return to him.
13 A rana ta fari ga wata na fari wanda Nuhu ya cika shekaru 601, ruwa ya shanye a ƙasa. Sai Nuhu ya buɗe murfin jirgin, ya ga cewa doron ƙasa ya bushe.
Noah was now 601 years old. By the first day of the first month [of the Jewish year], the water had completely drained away from the ground. Noah removed the covering on top of the ark, and he was surprised to see that the surface of the ground was drying.
14 A ran ashirin da bakwai ga wata na biyu, ƙasa ta bushe ƙaƙaf.
By the 27th day of the next month, the ground was completely dry.
15 Sa’an nan Allah ya ce wa Nuhu,
Then God said to Noah,
16 “Fito daga jirgin, kai da matarka da’ya’yanka maza da matansu.
“Leave the boat, along with your wife and your sons and their wives.
17 Ka fitar da kowane iri halitta mai rai da take tare da kai waje, tsuntsaye, dabbobi, da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa, don su yi ta haihuwa, su yi yawa, su ƙaru a duniya.”
Bring out with you all the birds, the animals, and all the creatures that scurry across the ground, in order that they can spread all over the earth and become very numerous.”
18 Sai Nuhu ya fito tare da matarsa da’ya’yansa maza da matan’ya’yansa,
So Noah left the boat, along with his wife and his sons and their wives.
19 da kowace irin dabba, da kowane mai rarrafe, da kowane irin tsuntsu, da kowane irin abu da yake tafiya a bisa duniya, suka fito daga jirgi daki-daki bisa ga irinsu.
And every kind of creature, including all those that scurry across the ground, all the birds, every creature that moves on the earth, left the boat. They left the boat in groups of their own species.
20 Sai Nuhu ya gina bagaden hadaya ga Ubangiji, ya ɗiba waɗansu dabbobi da tsuntsaye masu tsabta, ya yi hadaya ta ƙonawa da su a kan bagaden.
Then Noah built a (stone altar/place for offering sacrifices) to Yahweh. Then he took some of the animals that Yahweh had said were acceptable as sacrifices and killed them. Then he burned them whole on the altar.
21 Da Ubangiji ya ji ƙanshi mai daɗi, sai ya ce a zuciyarsa, “Ba zan ƙara la’anta ƙasa saboda mutum ba, ko da yake dukan tunanin zuciyar mutum mugu ne tun yana ƙarami. Ba kuwa zan ƙara hallaka dukan halittu masu rai, kamar yadda na yi ba.
When Yahweh smelled the pleasant odor, he was pleased with the sacrifice. Then he said to himself, “I will never again devastate everything on the earth because of the sinful things people do. Even though everything that people think is evil from the time they are young, I will not destroy all the living creatures again, as I did this time.
22 “Muddin duniya tana nan, lokacin shuki da na girbi, lokacin sanyi da na zafi, lokacin damina da na rani, dare da rana ba za su daina ba.”
As long as the earth exists, each year there will be seasons for planting seeds and seasons for harvesting crops. Each year there will be times when it is cold and times when it is hot, summer and winter (OR, rainy season and dry season). Each day there will be daytime and nighttime.”

< Farawa 8 >

A Dove is Sent Forth from the Ark
A Dove is Sent Forth from the Ark