< Farawa 43 >

1 A yanzu, yunwa ta yi tsanani a ƙasar.
Indlala yayilokhu inkulu kakhulu elizweni.
2 Saboda haka sa’ad da suka cinye dukan hatsin da suka kawo daga Masar, mahaifinsu ya ce musu, “Ku koma, ku sayo mana ƙarin abinci.”
Ngakho kwathi sebekuqedile konke ukudla ababekuthenge eGibhithe, uyise wathi kubo, “Buyelani liyesithengela njalo okunye ukudla okunenganyana.”
3 Amma Yahuda ya ce masa, “Mutumin ya gargaɗe mu sosai cewa, ‘Ba za ku sāke ganin fuskata ba sai in ɗan’uwanku yana tare da ku.’
Kodwa uJuda wathi kuye, “Indoda leyo yasiqonqosela yathi, ‘Ngeke liphinde libubone ubuso bami ngaphandle kokuba lilomnawenu.’
4 In za ka aika da ɗan’uwanmu tare da mu, za mu gangara mu sayo maka abinci.
Nxa uzamvumela umnawethu ukuthi sihambe laye, sizahamba siyekuthengela ukudla.
5 Amma in ba za ka aika da shi ba, ba za mu gangara ba, gama mutumin ya ce mana, ‘Ba za ku sāke ganin fuskata ba sai ko in ɗan’uwanku yana tare da ku.’”
Kodwa nxa ungezukuvuma, ngeke sibuyele, ngoba phela indoda leyo yathi kithi, ‘Ngeke liphinde libubone ubuso bami nxa umnawenu lingelaye.’”
6 Isra’ila ya yi tambaya, “Me ya sa kuka kawo wannan damuwa a kaina ta wurin faɗa wa mutumin cewa kuna da wani ɗan’uwa?”
U-Israyeli wabuza wathi, “Likwenzeleni lina ukungehlisela uhlupho lolu ngokuyitshela indoda leyo ukuthi lilomnawenu na?”
7 Suka amsa, “Mutumin ya yi mana tambaya sosai game da kanmu da iyalinmu. Ya tambaye mu, ‘Mahaifinku yana da rai har yanzu? Kuna da wani ɗan’uwa?’ Mu dai mun amsa tambayoyinsa ne. Ta yaya za mu sani zai ce, ‘Ku kawo ɗan’uwanku a nan’?”
Baphendula bathi, “Leyondoda isibuzisisile ngathi langendlu yangakithi yathi, ‘Uyihlo usaphila na? Lilaye na omunye umfowenu?’ Thina besiphendula imibuzo yayo kuphela. Sasingazi kanjani ukuthi yayizakuthi, ‘Mletheni umnawenu lapha’?”
8 Sa’an nan Yahuda ya ce wa Isra’ila mahaifinsa, “Ka aika saurayin tare da ni za mu kuwa tafi nan da nan, saboda mu da’ya’yanmu mu rayu, kada mu mutu.
UJuda wasesithi ku-Israyeli uyise, “Wothi umfana ahambe lami, sizahle sisuke nje masinyane, ukwenzela ukuthi thina lawe kanye labantwabethu siphile, singafi.
9 Ni kaina zan tabbatar da lafiyarsa; na ɗauki lamuninsa, a hannuna za ka neme shi. In ban dawo da shi gare ka, in sa shi nan a gabanka ba, zan ɗauki laifin a gabanka dukan kwanakina.
Mina ngokwami ngizazinikela ngokuphepha kwakhe; umlandu wonke ngaye awubekwe phezu kwami. Nxa ngingambuyisi kuwe ngimbeke phambi kwakho, ngizakuba lecala kuwe impilo yami yonke.
10 Ai, da ba mun jinkirta ba, da mun komo har sau biyu.”
Njengoba kunje nje, aluba asizilingananga ngabe sesihambe saphenduka kwaze kwaba kabili.”
11 Sa’an nan mahaifinsu Isra’ila ya ce musu, “In dole ne a yi haka, to, sai ku yi. Ku sa waɗansu amfani mafi kyau na ƙasar a buhunanku, ku ɗauka zuwa wurin mutumin a matsayin kyauta, da ɗan man ƙanshi na shafawa, da kuma’yar zuma, da kayan yaji, da ƙaro, da tsabar citta da kuma almon.
Ngakho uyise u-Israyeli wasesithi kubo, “Nxa kumele kube njalo, yenzani lokhu: Fakani emasakeni enu ezinye izinto ezinhle kakhulu eziphuma kulelilizwe lihambe lazo kulowomuntu zibe yisipho, amagcobo okuthambisa loluju, iziyoliso ezithile lemure, izilimo ezicacadwayo zephistakhiyo le-alimondi.
12 Ku ɗauki ninki biyu na yawan azurfa tare da ku, gama dole ku mayar da azurfan da aka sa a cikin bakunan buhunanku. Mai yiwuwa an yi haka a kuskure ne.
Thathani isiliva esiphindwe kabili, ngoba kufanele libuyisele lesosiliva esasibuyiselwe emasakeni enu. Mhlawumbe kwaba yisiphosiso.
13 Ku ɗauki ɗan’uwanku kuma ku koma wurin mutumin nan da nan.
Mthatheni umnawenu laye libuyele kuleyondoda ngokuphangisa.
14 Bari Allah Maɗaukaki yă nuna muku alheri a gaban mutumin saboda yă bar ɗan’uwanku da Benyamin su dawo tare da ku. Ni kuwa, in na yi rashi, na yi rashi.”
Sengathi uNkulunkulu uSomandla angalenzela umusa kuleyondoda ukuze ivumele omunye umfowenu kanye loBhenjamini baphenduke lani. Mina ngokwami ngithi, kambe okungayisikufa yikuphi!”
15 Saboda haka mutanen suka ɗauki kyautar, da kuma kuɗin da ya ninka na farko. Suka kuma ɗauki Benyamin, suka gaggauta suka gangara zuwa Masar suka kuma gabatar da kansu ga Yusuf.
Ngakho amadoda athatha izipho lesiliva esiphindwe kabili kanye loBhenjamini. Batshitsha baya eGibhithe bayazibika kuJosefa.
16 Sa’ad da Yusuf ya ga Benyamin tare da su, sai ya ce wa mai hidimar gidansa, “Ka shigar da mutanen cikin gida, ka yanka dabba ka shirya, gama mutanen za su ci abincin rana tare da ni.”
Kwathi uJosefa ebona uBhenjamini ekanye labo, wathi encekwini yendlu yakhe, “Hamba lamadoda la endlini yami, uwahlabele isifuyo ulungise ukudla; bazakudla lami emini.”
17 Mutumin ya yi kamar yadda Yusuf ya faɗa masa, ya kuwa ɗauki mutanen zuwa gidan Yusuf.
Indoda yenza njengokutshelwa kwayo nguJosefa, yawathatha amadoda yahamba lawo endlini kaJosefa.
18 Mutanen dai suka firgita sa’ad da aka ɗauke su zuwa gidansa. Suka yi tunani, “An kawo mu nan ne saboda azurfan da aka sa a cikin buhunanmu da farko. Yana so yă fāɗa mana, yă kuma sha ƙarfinmu, yă ƙwace mu kamar bayi, yă kuma kwashe jakunanmu.”
Amadoda ethuka ebona elethwa endlini kaJosefa. Bacabanga ukuthi, “Silethwe lapha ngenxa yesiliva esabuyiselwa emasakeni ethu ekufikeni kwethu kwakuqala. Ufuna ukusihlasela asehlule, abesesithumba sibe yizigqili athathe obabhemi bethu.”
19 Saboda haka suka je wurin mai yin wa Yusuf hidima, suka yi masa magana a bakin ƙofar gida.
Ngakho baya encekwini kaJosefa bayakhuluma laye entubeni eya endlini.
20 Suka ce, “Ranka yă daɗe, mun zo nan ƙaro na farko don mu saya abinci,
Bathi, “Ake usizwe, nkosi yethu: Safika lapha kuqala sizothenga ukudla.
21 amma a inda muka tsaya don mu kwana, da muka buɗe buhunanmu sai kowannenmu ya sami azurfansa daidai a bakin buhunsa. Saboda haka ga kuɗin a hannunmu, mun sāke komowa da su.
Kodwa lapho esaphumula khona ebusuku savula amasaka ethu, kwaba ngulowo wethu wafumana isiliva sakhe, siphelele ubunzima baso, sisemlonyeni wesaka lakhe. Ngakho size laso.
22 Mun kuma kawo ƙarin azurfa tare da mu don mu saya abinci. Ba mu san wa ya sa azurfanmu a cikin buhunanmu ba.”
Size lesinye isiliva phezu kwaleso ukuthi sithenge ukudla. Kasikwazi ukuthi ngubani owabuyisela isiliva emasakeni ethu.”
23 Sai mai hidimar ya ce, “Ba kome, kada ku ji tsoro. Allahnku, Allahn mahaifinku ne ya ba ku dukiyar a cikin buhunanku; ni dai, na karɓi azurfanku.” Sa’an nan ya fitar musu da Simeyon.
Wathi, “Kulungile. Lingesabi. UNkulunkulu wenu, uNkulunkulu kayihlo, uliphile inotho emasakeni enu; mina ngasiphiwa isiliva senu.” Emva kwalokho waseletha uSimiyoni kubo.
24 Mai yin hidimar ya ɗauki mutane zuwa gidan Yusuf ya ba su ruwa su wanke ƙafafunsu, ya kuma tanada wa jakunansu abinci.
Inceku yasiwangenisa amadoda endlini kaJosefa, yawapha amanzi okugeza inyawo zawo, yaletha lotshani babobabhemi bawo.
25 Suka shirya kyautansu domin isowar Yusuf da rana, gama sun ji cewa zai ci abinci a nan.
Balungisa izipho zabo balindela ukufika kukaJosefa emini ngoba basebezwile ukuthi babezakudla khonapho.
26 Sa’ad da Yusuf ya zo gida, sai suka ba shi kyautai da suka kawo, suka rusuna a gabansa har ƙasa.
UJosefa esefikile bethula izipho ababengene lazo endlini, njalo bakhothama kuye phansi.
27 Ya tambaye su, yaya suke, sa’an nan ya ce, “Yaya tsohon nan mahaifinku da kuka faɗa mini? Yana da rai har yanzu?”
Wababuza ukuphila, wasesithi, “Linjani ixhegu elinguyihlo elangitshela ngalo? Lilokhu lisaphila na?”
28 Suka amsa, “Bawanka mahaifinmu yana da rai har yanzu da kuma ƙoshin lafiya.” Suka kuma rusuna suka yi mubaya’a.
Baphendula bathi, “Inceku yakho, ubaba, ulokhu esaphila njalo usaqinile.” Bakhothama njalo betshengisa inhlonipho.
29 Da ya ɗaga idanu, sai ya ga ɗan’uwansa Benyamin, ɗan mahaifiyarsa, sai ya yi tambaya, “Wannan ne ƙaramin ɗan’uwanku, wanda kuka faɗa mini a kai?” Ya kuma ce, “Allah yă yi maka albarka, ɗana.”
Wathi elokhu ebakhangela wabona umnawakhe uBhenjamini, umntakanina sibili, wabuza wathi, “Nguye lo umnawenu olicinathunjana na, lowo elangitshela ngaye?” Wasesithi kuye, “UNkulunkulu kabe lomusa kuwe, ndodana yami.”
30 Saboda motsi mai zurfi da zuciyarsa ta yi da ganin ɗan’uwansa, sai Yusuf ya gaggauta ya fita, ya nemi wuri yă yi kuka. Ya shiga ɗakinsa ya yi kuka a can.
Wathinteka kakhulu ngokubona umnawakhe, uJosefa waphangisa waphuma wayafuna indawo yokukhala. Waya ekamelweni lakhe wayakhalela khona.
31 Bayan ya wanke fuskarsa, sai ya fito ya daure, ya umarta, “A kawo abinci.”
Wathi esegezile amehlo waphuma, wazibamba, wasesithi, “Phakululani ukudla.”
32 Sai aka raba musu abinci, nasa shi kaɗai su kuma su kaɗai, domin Masarawa ba sa cin abinci tare da Ibraniyawa, gama wannan abin ƙyama ne ga Masarawa.
Yena bamupha yedwa, abafowabo labo bodwa, kwathi lamaGibhithe ayesidla laye lawo aba wodwa, ngoba amaGibhithe ayengeke adla lamaHebheru, ngoba lokho kwakunengeka kumaGibhithe.
33 Aka zaunar da’yan’uwan Yusuf a gabansa bisa ga shekarunsu, daga ɗan fari zuwa auta.’Yan’uwan kuwa suka duddubi juna suna mamaki.
Amadoda la ayehlezi ngobudala bawo kuqala ngezibulo kusiyacina ngecinathunjana; bakhangelana bemangele.
34 Daga teburin da yake a gaban Yusuf aka riƙa ɗibar rabonsu ana kai musu, amma rabon Benyamin ya yi biyar ɗin na kowannensu. Suka kuwa sha, suka yi murna tare da shi.
Kwakusithi nxa bephakelwa kusuka etafuleni likaJosefa, isabelo sikaBhenjamini sasisedluliswa kahlanu kwesabanye. Ngakho bazitika banatha laye bekhululekile.

< Farawa 43 >