< Farawa 4 >

1 Adamu ya kwana da matarsa Hawwa’u, ta kuwa yi ciki ta haifi Kayinu. Sai ta ce, “Da taimakon Ubangiji na sami ɗa namiji.”
Y el varón tuvo relaciones con su mujer Eva, y quedó encinta, y dio a luz a Caín, y dijo: Me ha dado un hombre él Señor.
2 Daga baya ta haifi ɗan’uwansa, ta kuma ba shi suna Habila. Sa’ad da suka yi girma sai Habila ya zama makiyayin tumaki, Kayinu kuwa ya zama manomi.
Entonces ella volvió a tener un hijo y dio a luz a Abel, su hermano. Y Abel era pastor de ovejas, pero Caín era granjero.
3 Ana nan sai Kayinu ya kawo waɗansu amfanin gona a matsayin hadaya ga Ubangiji.
Y después de un tiempo, Caín le dio al Señor una ofrenda de los frutos de la tierra.
4 Amma Habila ya kawo mafi kyau daga’ya’yan fari na garkensa. Ubangiji ya yi farin ciki da sadakar da Habila ya kawo,
Y Abel dio una ofrenda de los corderos de su rebaño y de su grasa. Y el Señor estaba complacido con la ofrenda de Abel;
5 amma bai yi farin ciki da sadakar da Kayinu ya kawo ba. Saboda haka Kayinu ya ji fushi sosai, fuskarsa kuma ta ɓace.
Pero en Caín y en su ofrenda no se complació. Y Caín estaba enojado y su rostro se puso triste.
6 Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Don me kake fushi? Don me fuskarka ta ɓace?
Y él Señor dijo a Caín: ¿Por qué estás enojado? y por qué tu cara está triste?
7 Da ka yi abin da yake daidai, ai, da ka sami karɓuwa. Amma tun da ba ka yi abin da ba daidai ba, zunubi zai yi fakonka don yă rinjaye ka kamar naman jeji. Yana so yă mallake ka, amma tilas ka rinjaye shi.”
Si lo haces bien, ¿no tendrás honor? y si lo haces mal, el pecado te espera en la puerta, deseando tenerte, pero no dejes que sea tu amo.
8 To, Kayinu ya ce wa ɗan’uwansa Habila, “Mu tafi gona.” Yayinda suke a gona, sai Kayinu ya tasar wa Habila ya buge shi ya kashe.
Y dijo Caín a su hermano: Pasemos al campo; y estando ellos en el campo, Caín atacó a su hermano Abel y lo mató.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Ina ɗan’uwanka Habila?” Sai Kayinu ya ce, “Ban sani ba, ni mai gadin ɗan’uwana ne?”
Y él Señor dijo a Caín: ¿Dónde está tu hermano Abel? Y él dijo: No tengo idea: ¿soy el guardián de mi hermano?
10 Ubangiji ya ce, “Me ke nan ka yi? Saurara! Ga jinin ɗan’uwanka yana mini kuka daga ƙasa.
Y él dijo: ¿Qué has hecho? la voz de la sangre de tu hermano me está llamando desde la tierra.
11 Yanzu, kai la’ananne ne, an kuma kore ka daga ƙasa wadda ta buɗe bakinta ta shanye jinin ɗan’uwanka daga hannunka.
Y ahora eres maldito de la tierra, cuya boca está abierta para recibir la sangre de tu hermano de tu mano;
12 In ka nome ƙasa, ba za tă ƙara ba ka hatsinta ba. Za ka kuma zama mai yawo barkatai a duniya.”
La tierra ya no te dará su fruto como la recompensa de tu trabajo; serás un vagabundo errante sobre la tierra.
13 Kayinu ya ce wa Ubangiji, “Horon nan ya sha ƙarfina.
Y dijo Caín: Mi castigo es mayor que mi fuerza.
14 Ga shi, yau kana kori na daga ƙasar, zan zama a ɓoye daga fuskarka, zan kuma zama mai yawo barkatai, duk wanda ya same ni kuwa zai kashe ni.”
Me has enviado hoy de la faz de la tierra y de delante de tu rostro; Voy a ser un vagabundo errante sobre la tierra, y el que me vea me matará.
15 Amma Ubangiji ya ce masa, “Ba haka ba ne! Duk wanda ya kashe Kayinu, za a ninƙa hukuncinsa har sau bakwai.” Sa’an nan Ubangiji ya sa wa Kayinu alama don duk wanda ya same shi kada yă kashe shi.
Y él Señor dijo: De cierto, si muere Caín, siete vidas serán tomadas por él. Y el Señor puso una marca en Caín para que nadie lo matara.
16 Saboda haka Kayinu ya yi tafiyarsa ya rabu da Ubangiji, ya je ya zauna ƙasar Nod a gabashin Eden.
Y se apartó Caín de delante de la faz del Señor, y se quedó a vivir en la tierra de Nod, al oriente del Edén.
17 Kayinu ya kwana da matarsa, ta kuwa yi ciki, ta haifi Enok. A lokacin Kayinu yana gina birni, sai ya sa wa birnin sunan ɗansa Enok.
Y Caín tuvo relaciones con su esposa, y ella engendró y dio a luz a Enoc; y él hizo una ciudad, y le dio a la ciudad el nombre de Enoc por su hijo.
18 Aka haifa wa Enok Irad, Irad kuma ya haifi Mehujayel, Mehujayel kuma ya haifi Metushayel, Metushayel kuma ya haifin Lamek.
Y Enoc tuvo un hijo Irad; e Irad fue padre de Mehujael; y Mehujael padre de Metusael; y Metusael fue padre de Lamec.
19 Lamek ya auri mata biyu, ana ce da ɗaya Ada, ɗayan kuma Zilla.
Y Lamec tuvo dos mujeres; el nombre de uno era Ada, y el nombre del otro Zila.
20 Ada ta haifi Yabal, shi ne mahaifi waɗanda suke zama a tentuna, suna kuma kiwon dabbobi.
Y Ada dio a luz a Jabal; era el padre de los que viven en tiendas y tienen ganado.
21 Sunan ɗan’uwansa Yubal, shi ne mahaifin dukan makaɗan garaya da masu hura sarewa.
Y el nombre de su hermano era Jubal: él era el padre de todos los que tocan con arpa y flauta.
22 Zilla ma ta haifi ɗa, Tubal-Kayinu, shi ne wanda ya ƙera kowane iri kayan aiki daga tagulla da kuma ƙarfe.’Yar’uwar Tubal-Kayinu ita ce Na’ama.
Y Zila dio a luz a Tubal-caín, que es el padre de todo fabricante de instrumentos de bronce y de hierro, y la hermana de Tubal-caín fue Naama.
23 Wata rana, Lamek ya ce wa matansa, Ada da Zilla, “Ku saurara, matan Lamek, ku ji maganata. Na kashe wani saboda ya yi mini rauni, na kashe wani saurayi saboda ya ji mini ciwo.
Y dijo Lamec a sus mujeres, Ada y Zila, escucha mi voz; esposas de Lamec, presten atención a mis palabras, porque yo pondría a muerte a un hombre por una herida, y a un joven por un golpe;
24 Idan za a rama wa Kayinu har sau bakwai, lalle za a rama wa Lamek sau saba’in da bakwai ke nan.”
Si se quieren tomar siete vidas como castigo por la muerte de Caín, setenta y siete serán tomadas por las de Lamec.
25 Sai Adamu ya sāke kwana da matarsa, ta haifi ɗa, aka kuma ba shi suna Set, gama ta ce, “Allah ya ba ni wani yaro a madadin Habila, tun da yake Kayinu ya kashe shi.”
Y Adán volvió a tener relaciones con su esposa, y ella dio a luz a un hijo al que dio el nombre de Set, porque ella dijo: Dios me ha dado otra simiente en lugar de Abel, a quien Caín mató.
26 Set ma ya haifi ɗa, ya kuma kira shi Enosh. A lokaci ne, mutane suka fara kira ga sunan Ubangiji.
Y Set tuvo un hijo, y le dio el nombre de Enós: en este tiempo los hombres primero hicieron uso del nombre del Señor en adoración.

< Farawa 4 >