< Farawa 4 >

1 Adamu ya kwana da matarsa Hawwa’u, ta kuwa yi ciki ta haifi Kayinu. Sai ta ce, “Da taimakon Ubangiji na sami ɗa namiji.”
有一日,那人和他妻子夏娃同房,夏娃就怀孕,生了该隐,便说:“耶和华使我得了一个男子。”
2 Daga baya ta haifi ɗan’uwansa, ta kuma ba shi suna Habila. Sa’ad da suka yi girma sai Habila ya zama makiyayin tumaki, Kayinu kuwa ya zama manomi.
又生了该隐的兄弟亚伯。亚伯是牧羊的;该隐是种地的。
3 Ana nan sai Kayinu ya kawo waɗansu amfanin gona a matsayin hadaya ga Ubangiji.
有一日,该隐拿地里的出产为供物献给耶和华;
4 Amma Habila ya kawo mafi kyau daga’ya’yan fari na garkensa. Ubangiji ya yi farin ciki da sadakar da Habila ya kawo,
亚伯也将他羊群中头生的和羊的脂油献上。耶和华看中了亚伯和他的供物,
5 amma bai yi farin ciki da sadakar da Kayinu ya kawo ba. Saboda haka Kayinu ya ji fushi sosai, fuskarsa kuma ta ɓace.
只是看不中该隐和他的供物。该隐就大大地发怒,变了脸色。
6 Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Don me kake fushi? Don me fuskarka ta ɓace?
耶和华对该隐说:“你为什么发怒呢?你为什么变了脸色呢?
7 Da ka yi abin da yake daidai, ai, da ka sami karɓuwa. Amma tun da ba ka yi abin da ba daidai ba, zunubi zai yi fakonka don yă rinjaye ka kamar naman jeji. Yana so yă mallake ka, amma tilas ka rinjaye shi.”
你若行得好,岂不蒙悦纳?你若行得不好,罪就伏在门前。它必恋慕你,你却要制伏它。”
8 To, Kayinu ya ce wa ɗan’uwansa Habila, “Mu tafi gona.” Yayinda suke a gona, sai Kayinu ya tasar wa Habila ya buge shi ya kashe.
该隐与他兄弟亚伯说话;二人正在田间。该隐起来打他兄弟亚伯,把他杀了。
9 Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Ina ɗan’uwanka Habila?” Sai Kayinu ya ce, “Ban sani ba, ni mai gadin ɗan’uwana ne?”
耶和华对该隐说:“你兄弟亚伯在哪里?”他说:“我不知道!我岂是看守我兄弟的吗?”
10 Ubangiji ya ce, “Me ke nan ka yi? Saurara! Ga jinin ɗan’uwanka yana mini kuka daga ƙasa.
耶和华说:“你做了什么事呢?你兄弟的血有声音从地里向我哀告。
11 Yanzu, kai la’ananne ne, an kuma kore ka daga ƙasa wadda ta buɗe bakinta ta shanye jinin ɗan’uwanka daga hannunka.
地开了口,从你手里接受你兄弟的血。现在你必从这地受咒诅。
12 In ka nome ƙasa, ba za tă ƙara ba ka hatsinta ba. Za ka kuma zama mai yawo barkatai a duniya.”
你种地,地不再给你效力;你必流离飘荡在地上。”
13 Kayinu ya ce wa Ubangiji, “Horon nan ya sha ƙarfina.
该隐对耶和华说:“我的刑罚太重,过于我所能当的。
14 Ga shi, yau kana kori na daga ƙasar, zan zama a ɓoye daga fuskarka, zan kuma zama mai yawo barkatai, duk wanda ya same ni kuwa zai kashe ni.”
你如今赶逐我离开这地,以致不见你面;我必流离飘荡在地上,凡遇见我的必杀我。”
15 Amma Ubangiji ya ce masa, “Ba haka ba ne! Duk wanda ya kashe Kayinu, za a ninƙa hukuncinsa har sau bakwai.” Sa’an nan Ubangiji ya sa wa Kayinu alama don duk wanda ya same shi kada yă kashe shi.
耶和华对他说:“凡杀该隐的,必遭报七倍。”耶和华就给该隐立一个记号,免得人遇见他就杀他。
16 Saboda haka Kayinu ya yi tafiyarsa ya rabu da Ubangiji, ya je ya zauna ƙasar Nod a gabashin Eden.
于是该隐离开耶和华的面,去住在伊甸东边挪得之地。
17 Kayinu ya kwana da matarsa, ta kuwa yi ciki, ta haifi Enok. A lokacin Kayinu yana gina birni, sai ya sa wa birnin sunan ɗansa Enok.
该隐与妻子同房,他妻子就怀孕,生了以诺。该隐建造了一座城,就按着他儿子的名将那城叫做以诺。
18 Aka haifa wa Enok Irad, Irad kuma ya haifi Mehujayel, Mehujayel kuma ya haifi Metushayel, Metushayel kuma ya haifin Lamek.
以诺生以拿;以拿生米户雅利;米户雅利生玛土撒利;玛土撒利生拉麦。
19 Lamek ya auri mata biyu, ana ce da ɗaya Ada, ɗayan kuma Zilla.
拉麦娶了两个妻:一个名叫亚大,一个名叫洗拉。
20 Ada ta haifi Yabal, shi ne mahaifi waɗanda suke zama a tentuna, suna kuma kiwon dabbobi.
亚大生雅八;雅八就是住帐棚、牧养牲畜之人的祖师。
21 Sunan ɗan’uwansa Yubal, shi ne mahaifin dukan makaɗan garaya da masu hura sarewa.
雅八的兄弟名叫犹八;他是一切弹琴吹箫之人的祖师。
22 Zilla ma ta haifi ɗa, Tubal-Kayinu, shi ne wanda ya ƙera kowane iri kayan aiki daga tagulla da kuma ƙarfe.’Yar’uwar Tubal-Kayinu ita ce Na’ama.
洗拉又生了土八·该隐;他是打造各样铜铁利器的。土八·该隐的妹子是拿玛。
23 Wata rana, Lamek ya ce wa matansa, Ada da Zilla, “Ku saurara, matan Lamek, ku ji maganata. Na kashe wani saboda ya yi mini rauni, na kashe wani saurayi saboda ya ji mini ciwo.
拉麦对他两个妻子说: 亚大、洗拉,听我的声音; 拉麦的妻子,细听我的话语: 壮年人伤我,我把他杀了; 少年人损我,我把他害了。
24 Idan za a rama wa Kayinu har sau bakwai, lalle za a rama wa Lamek sau saba’in da bakwai ke nan.”
若杀该隐,遭报七倍, 杀拉麦,必遭报七十七倍。
25 Sai Adamu ya sāke kwana da matarsa, ta haifi ɗa, aka kuma ba shi suna Set, gama ta ce, “Allah ya ba ni wani yaro a madadin Habila, tun da yake Kayinu ya kashe shi.”
亚当又与妻子同房,她就生了一个儿子,起名叫塞特,意思说:“神另给我立了一个儿子代替亚伯,因为该隐杀了他。”
26 Set ma ya haifi ɗa, ya kuma kira shi Enosh. A lokaci ne, mutane suka fara kira ga sunan Ubangiji.
塞特也生了一个儿子,起名叫以挪士。那时候,人才求告耶和华的名。

< Farawa 4 >