< Farawa 34 >

1 To, Dina,’yar da Liyatu ta haifa wa Yaƙub, ta je ta ziyarci matan ƙasar.
پس دینه، دختر لیه، که او را برای یعقوب زاییده بود، برای دیدن دختران آن ملک بیرون رفت.۱
2 Sa’ad da Shekem ɗan Hamor Bahiwiye mai mulkin wurin ya gan ta, sai ya kama ta, ya kwana da ita, ya ɓata ta.
و چون شکیم بن حمورحوی که رئیس آن زمین بود، او را بدید، او را بگرفت و با او همخواب شده، وی را بی‌عصمت ساخت.۲
3 Zuciyarsa kuwa ta damu da son Dina’yar Yaƙub, ya kuwa ƙaunaci yarinyar, ya yi mata magana a hankali.
و دلش به دینه، دختر یعقوب، بسته شده، عاشق آن دختر گشت، و سخنان دل آویز به آن دختر گفت.۳
4 Sai Shekem ya ce wa mahaifinsa Hamor, “Ka auro mini wannan yarinya ta zama matata.”
و شکیم به پدر خود، حمورخطاب کرده، گفت: «این دختر را برای من به زنی بگیر.»۴
5 Sa’ad da Yaƙub ya ji cewa an ɓata’yarsa Dina, sai ya yi shiru game da batun sai’ya’yansa maza sun dawo gida, gama’ya’yansa suna a jeji tare da dabbobinsa suna kiwo.
و یعقوب شنید که دخترش دینه رابی عصمت کرده است. و چون پسرانش با مواشی او در صحرا بودند، یعقوب سکوت کرد تا ایشان بیایند.۵
6 Sai Hamor mahaifin Shekem ya je don yă yi magana da Yaƙub.
و حمور، پدر شکیم نزد یعقوب بیرون آمد تا به وی سخن گوید.۶
7 Da’ya’yan Yaƙub maza suka dawo daga jeji sai suka ji labarin. Abin kuwa ya zafe su ƙwarai, don Shekem ya jawo abin kunya wa jama’ar Isra’ila ta wurin kwana da’yar Yaƙub, don bai kamata wannan abu yă faru ba.
و چون پسران یعقوب این را شنیدند، از صحرا آمدند و غضبناک شده، خشم ایشان به شدت افروخته شد، زیرا که بادختر یعقوب همخواب شده، قباحتی دراسرائیل نموده بود و این عمل، ناکردنی بود.۷
8 Amma Hamor ya ce musu, “Ɗana Shekem ya sa zuciyarsa a kan’yarku. Ina roƙonku ku ba shi ita yă aura.
پس حمور ایشان را خطاب کرده، گفت: «دل پسرم شکیم شیفته دختر شماست؛ او را به وی به زنی بدهید.۸
9 Ku yi auratayya da mu; ku aurar mana da’ya’yanku mata, ku kuma ku auro’ya’yanmu mata wa kanku.
و با ما مصاهرت نموده، دختران خود را به ما بدهید و دختران ما را برای خودبگیرید.۹
10 Za ku iya zauna a cikinmu, ƙasar tana nan a buɗe dominku. Ku yi zama a cikinta, ku yi sana’a, ku kuma sami dukiya.”
و با ما ساکن شوید و زمین از آن شماباشد. در آن بمانید و تجارت کنید و در آن تصرف کنید.»۱۰
11 Sai Shekem ya ce wa mahaifin Dina da kuma’yan’uwanta. “Bari in sami tagomashi a idanunku, zan kuwa ba ku duk abin da kuka tambaya.
و شکیم به پدر و برادران آن دختر گفت: «در نظر خود مرا منظور بدارید و آنچه به من بگویید، خواهم داد.۱۱
12 Ku faɗa mini nawa ne dukiyar aure da kuma sadakin da zan kawo bisa ga yadda kuke so, zan kuwa biya duk abin da kuka ce. Ku dai bar ni in aure yarinyar ta zama matata.”
مهر و پیشکش هر قدرزیاده از من بخواهید، آنچه بگویید، خواهم دادفقط دختر را به زنی به من بسپارید.»۱۲
13 Domin an ɓata’yar’uwansu Dina, sai’ya’yan Yaƙub maza suka amsa a ha’ince yayinda suke wa Shekem da mahaifinsa Hamor magana.
اما پسران یعقوب در جواب شکیم و پدرش حمور به مکرسخن‌گفتند زیرا خواهر ایشان، دینه رابی عصمت کرده بود.۱۳
14 Suka ce musu, “Ba za mu iya yin wannan abu ba, ba za mu iya ba da’yar’uwarmu ga mutumin da ba shi da kaciya ba. Wannan zai zama abin kunya ne a gare mu.
پس بدیشان گفتند: «این کار را نمی توانیم کرد که خواهر خود را به شخصی نامختون بدهیم، چونکه این برای ما ننگ است.۱۴
15 Za mu yarda da wannan kaɗai ta wannan sharaɗi, cewa za ku zama kamar mu ta wurin yin wa dukan’ya’yanku maza kaciya.
لکن بدین شرط با شما همداستان می‌شویم اگر چون ما بشوید، که هر ذکوری ازشما مختون گردد.۱۵
16 Sa’an nan za mu ba da’ya’yanmu mata aure gare ku, mu kuma mu aure’ya’yanku mata wa kanmu. Za mu zauna a cikinku mu kuma zama mutane ɗaya da ku.
آنگاه دختران خود را به شما دهیم و دختران شما را برای خود گیریم و باشما ساکن شده، یک قوم شویم.۱۶
17 Amma in ba za ku yarda a yi muku kaciya ba, za mu ɗauki’yar’uwanmu mu tafi.”
اما اگر سخن ما را اجابت نکنید و مختون نشوید، دختر خود رابرداشته، از اینجا کوچ خواهیم کرد.»۱۷
18 Sharuɗansu sun gamshi Hamor da ɗansa, Shekem.
و سخنان ایشان بنظر حمور و بنظر شکیم بن حمور پسند افتاد.۱۸
19 Saurayin wanda aka fi girmamawa a cikin dukan gidan mahaifinsa, bai ɓata lokaci a yin abin da suka ce ba, domin ya ji daɗin’yar Yaƙub.
و آن جوان در کردن این کار تاخیر ننمود، زیرا که شیفته دختر یعقوب بود، و او از همه اهل خانه پدرش گرامی تر بود.۱۹
20 Saboda haka Hamor da ɗansa Shekem suka tafi ƙofar birninsu don su yi magana da mutanen garinsu.
پس حمور و پسرش شکیم به دروازه شهرخود آمده، مردمان شهر خود را خطاب کرده، گفتند:۲۰
21 Suka ce, “Waɗannan mutane ba su da damuwa, bari su zauna a cikin ƙasarmu, su kuma yi sana’a a ciki; ƙasar tana da isashen fili dominsu. Za mu iya auro’ya’yansu mata, su kuma su auri namu.
«این مردمان با ما صلاح اندیش هستند، پس در این زمین ساکن بشوند، و در آن تجارت کنند. اینک زمین از هر طرف برای ایشان وسیع است؛ دختران ایشان را به زنی بگیریم و دختران خود را بدیشان بدهیم.۲۱
22 Amma mutanen za su yarda su zauna tare da mu kamar mutane ɗaya kawai bisa wannan sharaɗi, cewa a yi wa mazanmu kaciya, kamar yadda su kansu suke.
فقط بدین شرط ایشان باما متفق خواهند شد تا با ما ساکن شده، یک قوم شویم که هر ذکوری از ما مختون شود، چنانکه ایشان مختونند.۲۲
23 Ashe, shanunsu, dukiyarsu da dukan sauran dabbobinsu, ba za su zama namu ba? Saboda haka mu yarda, za su kuwa zauna a cikinmu.”
آیا مواشی ایشان و اموال ایشان و هر حیوانی که دارند، از آن ما نمی شود؟ فقط با ایشان همداستان شویم تا با ما ساکن شوند.»۲۳
24 Dukan mazan da suka fito ƙofar birnin suka yarda da Hamor da kuma ɗansa Shekem, aka kuwa yi wa kowane namiji a birnin kaciya.
پس همه کسانی که به دروازه شهر اودرآمدند، به سخن حمور و پسرش شکیم رضادادند، و هر ذکوری از آنانی که به دروازه شهر اودرآمدند، مختون شدند.۲۴
25 Bayan kwana uku, yayinda dukansu suna cikin zafi mikin kaciya, sai biyu daga cikin’ya’yan Yaƙub maza, Simeyon da Lawi,’yan’uwan Dina, suka ɗauki takubansu suka fāɗa wa birnin ba labari, suka kashe kowane namiji.
و در روز سوم چون دردمند بودند، دو پسر یعقوب، شمعون و لاوی، برادران دینه، هر یکی شمشیر خود را گرفته، دلیرانه بر شهر آمدند و همه مردان را کشتند.۲۵
26 Suka kashe Hamor da ɗansa Shekem da takobi, suka ɗauko Dina daga gidan Shekem suka tafi.
وحمور و پسرش شکیم را به دم شمشیر کشتند، ودینه را از خانه شکیم برداشته، بیرون آمدند.۲۶
27 Sa’an nan’ya’yan Yaƙub maza suka bi kan gawawwakin, suka washe arzikin birni saboda an ɓata’yar’uwarsu.
وپسران یعقوب بر کشتگان آمده، شهر را غارت کردند، زیرا خواهر ایشان را بی‌عصمت کرده بودند.۲۷
28 Suka kwashe garkunansu na shanu da jakuna, da kuma kome na mutanen a birnin da kuma cikin gonaki.
و گله‌ها و رمه‌ها و الاغها و آنچه در شهرو آنچه در صحرا بود، گرفتند.۲۸
29 Suka kwashe dukan dukiyarsu da dukan matansu da’ya’yansu, suka kwashe kome da yake cikin gidaje.
و تمامی اموال ایشان و همه اطفال و زنان ایشان را به اسیری بردند. و آنچه در خانه‌ها بود تاراج کردند.۲۹
30 Sai Yaƙub ya ce wa Simeyon da Lawi, “Kun jawo mini wahala ta wurin sa in zama abin ƙi ga Kan’aniyawa da Ferizziyawa, mazaunan wannan ƙasa. Mu kima ne, in kuwa suka haɗa kai gāba da ni, suka fāɗa mini, za su hallaka ni da gidana.”
پس یعقوب به شمعون و لاوی گفت: «مرا به اضطراب انداختید، و مرا نزد سکنه این زمین، یعنی کنعانیان و فرزیان مکروه ساختید، و من در شماره قلیلم، همانا بر من جمع شوند و مرا بزنند و من با خانه‌ام هلاک شوم.»۳۰
31 Amma’ya’yansa suka amsa, “To, ya dace ke nan da ya yi da’yar’uwarmu kamar karuwa?”
گفتند: «آیا او با خواهر ما مثل فاحشه عمل کند؟»۳۱

< Farawa 34 >