< Farawa 32 >
1 Yaƙub shi ma ya kama hanyarsa, sai mala’ikun Allah suka sadu da shi.
And Jacob went on his way, and the agents of God met him.
2 Sa’ad da Yaƙub ya gan su sai ya ce, “Wannan sansanin Allah ne!” Saboda haka ya kira wannan wuri Mahanayim.
And Jacob said when he saw them, This is God's camp. And he called the name of that place Mahanaim.
3 Sai Yaƙub ya aiki manzanni su sha gabansa zuwa wurin ɗan’uwansa Isuwa a ƙasar Seyir, a ƙauyen Edom.
And Jacob sent messengers before him to Esau his brother to the land of Seir, the field of Edom.
4 Ya umarce su, “Ga abin da za ku faɗa wa maigidana Isuwa, ‘Bawanka Yaƙub ya ce, na yi zama tare da Laban na kuwa kasance a can sai yanzu.
And he commanded them, saying, Thus shall ye say to my lord Esau, Thus says thy servant Jacob, I have sojourned with Laban, and stayed until now.
5 Ina da shanu da jakuna, tumaki da awaki, bayi maza da mata. Yanzu ina aika da wannan saƙo zuwa ga ranka yă daɗe, don in sami tagomashi a idanunka.’”
And I have oxen, and donkeys, flocks, and men-servants, and maid-servants. And I have sent to tell my lord, that I may find favor in thy sight.
6 Sa’ad da manzannin suka komo wurin Yaƙub, suka ce, “Mun tafi wurin ɗan’uwanka Isuwa, yanzu kuwa yana zuwa ya sadu da kai, da kuma mutum ɗari huɗu tare da shi.”
And the messengers returned to Jacob, saying, We came to thy brother Esau, and moreover he comes to meet thee, and four hundred men with him.
7 Da tsoro mai yawa da kuma damuwa, Yaƙub ya rarraba mutanen da suke tare da shi ƙungiyoyi biyu, haka ma garkunan tumaki da awaki, da garkunan shanu da raƙuma.
Then Jacob was greatly afraid and was distressed. And he divided the people that were with him, and the flocks, and the herds, and the camels, into two companies.
8 Ya yi tunani, “In Isuwa ya zo ya fāɗa wa ƙungiya ɗaya, sai ƙungiya ɗayan da ta ragu ta tsira.”
And he said, If Esau comes to the one company, and smites it, then the company which is left shall escape.
9 Sa’an nan Yaƙub ya yi addu’a, “Ya Allah na mahaifina Ibrahim, Allah na mahaifina Ishaku. Ya Ubangiji kai da ka ce mini, ‘Koma ƙasarka zuwa wurin danginka, zan kuma sa ka yi albarka.’
And Jacob said, O God of my father Abraham, and God of my father Isaac, O Jehovah, who said to me, Return to thy country, and to thy kindred, and I will do thee good,
10 Ban cancanci dukan alheri da amincin da ka nuna wa bawanka ba. Da sanda kaɗai nake sa’ad da na ƙetare wannan Urdun, amma ga shi yanzu na zama ƙungiyoyi biyu.
I am not worthy of the least of all the loving kindnesses, and of all the truth, which thou have shown to thy servant, for with my staff I passed over this Jordan, and now I have become two companies.
11 Ka cece ni, ina roƙonka daga hannun ɗan’uwana Isuwa, gama ina tsoro zai zo yă fāɗa mini, yă karkashe mu duka,’ya’ya da iyaye.
Deliver me, I pray thee, from the hand of my brother, from the hand of Esau. For I fear him, lest he comes and smites me, the mother with the sons.
12 Amma ka riga ka faɗa, ‘Tabbatacce zan sa ka yi albarka. Zan kuma sa zuriyarka su zama kamar yashin teku da ba a iya ƙirgawa.’”
And thou said, I will surely do thee good, and make thy seed as the sand of the sea, which cannot be numbered for multitude.
13 Ya kwana a can, daga cikin abin da yake tare da shi kuwa, ya zaɓi kyauta domin ɗan’uwansa Isuwa,
And he lodged there that night, and took of that which he had with him a present for Esau his brother:
14 awaki ɗari biyu da bunsurai ashirin, tumaki ɗari biyu da raguna ashirin,
two hundred she-goats and twenty he-goats, two hundred ewes and twenty rams,
15 raƙuma mata talatin tare da ƙananansu, shanu arba’in da bijimai goma, jakuna mata ashirin da kuma jakuna maza goma.
thirty milk camels and their colts, forty cows and ten bulls, twenty she-donkeys and ten foals.
16 Ya sa su a ƙarƙashin kulawar bayinsa, kowane kashin garke ya kasance a ware. Ya ce wa bayinsa, “Ku sha gabana, ku kuma ba da rata tsakanin garke da garke.”
And he delivered them into the hand of his servants, every herd by itself, and said to his servants, Pass over before me, and put a space between herd and herd.
17 Ya umarci wanda yake jagorar ya ce, “Sa’ad da ɗan’uwana Isuwa ya sadu da ku ya kuma yi tambaya, ‘Ku na wane ne, ina za ku, kuma wane ne mai dukan dabbobin nan da suke gabanku?’
And he commanded the foremost, saying, When Esau my brother meets thee, and asks thee, saying, Whose are thou? And where do thou go? And whose are these before thee?
18 Sai ku ce, ‘Na bawanka Yaƙub ne. Kyauta ce wa maigidana Isuwa, yana kuma tafe a bayanmu.’”
Then thou shall say, Thy servant Jacob's. It is a present sent to my lord Esau. And, behold, he also is behind us.
19 Yaƙub ya kuma umarci na biyu da na uku da kuma dukan waɗansu da suka bi garkunan, “Sai ku faɗa irin abu guda ga Isuwa sa’ad da kuka sadu da shi.
And he commanded also the second, and the third, and all who followed the herds, saying, On this manner shall ye speak to Esau when ye find him,
20 Ku kuma tabbata kun ce, ‘Bawanka Yaƙub yana tafe a bayanmu.’” Gama Yaƙub ya yi tunani cewa, “Zan kwantar da ran Isuwa da waɗannan kyautai, kafin mu sadu fuska da fuska, wataƙila yă karɓe shi.”
and ye shall say, Moreover, behold, thy servant Jacob is behind us. For he said, I will appease him with the present that goes before me, and afterward I will see his face. Perhaps he will accept me.
21 Saboda haka kyautai Yaƙub suka sha gabansa, amma shi kansa ya kwana a sansani.
So the present passed over before him, and he himself lodged that night in the company.
22 A wannan dare Yaƙub ya tashi ya ɗauki matansa biyu, da matan nan biyu masu hidima da’ya’yansa goma sha ɗaya ya haye rafin Yabbok.
And he rose up that night, and took his two wives, and his two handmaids, and his eleven sons, and passed over the ford of the Jabbok.
23 Bayan ya sa suka haye rafin, haka ma ya tura dukan mallakarsa zuwa hayen.
And he took them, and sent them over the stream, and sent over that which he had.
24 Saboda haka sai aka bar Yaƙub shi kaɗai. Sai ga wani mutum ya zo ya yi kokawa da shi har wayewar gari.
And Jacob was left alone, and a man wrestled with him until the breaking of the day.
25 Da mutumin ya ga cewa bai fi ƙarfin Yaƙub ba, sai ya bugi kwarin ƙashin cinyar Yaƙub, sai gaɓar ƙashin cinyarsa ya goce, a sa’ad da yake kokawa da mutumin.
And when he saw that he did not prevail against him, he touched the hollow of his thigh, and the hollow of Jacob's thigh was strained as he wrestled with him.
26 Sa’an nan mutumin ya ce, “Bar ni in tafi, gama gari ya waye.” Amma Yaƙub ya amsa ya ce, “Ba zan bar ka ka tafi ba, sai ka sa mini albarka.”
And he said, Let me go, for the day breaks. And he said, I will not let thee go unless thou bless me.
27 Mutumin ya tambaye shi ya ce, “Mene ne sunanka?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Yaƙub.”
And he said to him, What is thy name? And he said, Jacob.
28 Sai mutumin ya ce, “Sunanka ba zai ƙara zama Yaƙub ba, amma Isra’ila, gama ka yi kokawa da Allah da mutane, ka kuwa yi rinjaye.”
And he said, Thy name shall no more be called Jacob, but Israel, for thou have striven with God and with men, and have prevailed.
29 Yaƙub ya ce, “Ina roƙonka, faɗa mini sunanka.” Amma mutumin ya amsa ya ce, “Me ya sa kake tambayata sunana?” Sa’an nan ya albarkace shi.
And Jacob asked him, and said, Tell me, I pray thee, thy name. And he said, Why is it that thou ask for my name? And he blessed him there.
30 Saboda haka Yaƙub ya kira wurin Feniyel, yana cewa, “Domin na ga Allah fuska da fuska, duk da haka aka bar ni da rai.”
And Jacob called the name of the place Peniel, for, I have seen God face to face, and my life is preserved.
31 Rana ta yi sama a sa’ad da ya wuce Fenuwel yana kuma ɗingishi saboda ƙashin cinyarsa.
And the sun rose upon him as he passed over Penuel, and he limped upon his thigh.
32 Wannan ya sa har wa yau Isra’ilawa ba sa cin jijiyar ƙashin cinya wadda take a kwarin ƙashin cinya, domin an taɓa kwarin ƙashin cinyar Yaƙub kusa da jijiyar.
Therefore the sons of Israel do not eat the sinew of the hip which is upon the hollow of the thigh, to this day, because he touched the hollow of Jacob's thigh in the sinew of the hip.