< Farawa 3 >

1 To, maciji dai ya fi kowane a cikin namun jejin da Ubangiji Allah ya yi wayo. Ya ce wa macen, “Tabbatacce ne Allah ya ce, ‘Kada ku ci daga kowane itace a lambu’?”
Torej kača [pa] je bila bolj premetena kakor katerakoli izmed poljskih živali, ki jih je Gospod Bog naredil. In rekla je ženski: »Da, ali je Bog res rekel: ›Ne bosta jedla od vsakega vrtnega drevesa?‹«
2 Macen ta ce wa macijin, “Za mu iya ci daga’ya’ya itatuwa a lambun,
In ženska je rekla kači: »Midva lahko jeva od sadja vrtnih dreves,
3 amma Allah ya ce, ‘Kada ku ci daga’ya’yan itacen da yake tsakiyar lambu, kada kuma ku taɓa shi, in ba haka ba kuwa za ku mutu.’”
toda o sadu drevesa, ki je v sredi vrta, je Bog rekel: ›Ne bosta jedla od njega niti se ga ne bosta dotikala, da ne bi umrla.‹«
4 Maciji ya ce wa macen, “Tabbatacce ba za ku mutu ba.
Kača je ženski rekla: »Zagotovo ne bosta umrla,
5 Gama Allah ya san cewa sa’ad da kuka ci daga itacen idanunku za su buɗe, za ku kuma zama kamar Allah, ku san abin da yake mai kyau da abin da yake mugu.”
kajti Bog ve, da se bodo na dan, ko bosta od njega jedla, vajine oči potem odprle in bosta kakor bogovi, poznavajoč dobro in zlo.«
6 Sa’ad da macen ta ga’ya’yan itacen suna da kyau don abinci, abin sha’awa ga ido, abin marmari kuma don samun hikima, sai ta tsinka ta ci, ta kuma ba da waɗansu wa mijinta wanda yake tare da ita, shi ma ya ci.
In ko je ženska videla, da je bilo drevo dobro za jed in da je bilo prijetno očem in da si je drevesa želeti, da naredi nekoga modrega, je vzela od njegovega sadu in jedla ter dala tudi svojemu soprogu, [ki je bil] z njo, in on je jedel.
7 Sa’an nan idanun dukansu biyu suka buɗe, suka kuma gane tsirara suke; saboda haka suka ɗinɗinka ganyayen ɓaure suka yi wa kansu sutura.
Oči so se obema odprle in spoznala sta, da sta bila naga. Skupaj sta sešila figove liste ter si naredila predpasnika.
8 Da mutumin da matarsa suka ji motsin Ubangiji Allah yana takawa a lambun a sanyin yini, sai suka ɓuya daga Ubangiji Allah a cikin itatuwan lambu.
In zaslišala sta šum Gospoda Boga, ki je v svežini dneva hodil po vrtu, in Adam ter njegova žena sta se pred prisotnostjo Gospoda Boga skrila med vrtna drevesa.
9 Amma Ubangiji Allah ya kira mutumin ya ce, “Ina kake?”
Gospod Bog je zaklical Adamu in mu rekel: »Kje si?«
10 Ya ce, “Na ji ka a cikin lambu, na kuwa ji tsoro gama ina tsirara, saboda haka na ɓuya.”
Ta je rekel: »Zaslišal sem tvoj šum na vrtu in sem se zbal, ker sem bil nag, in sem se skril.«
11 Sai ya ce, “Wa ya faɗa maka cewa kana tsirara? Ko dai ka ci daga itacen da na umarce ka kada ka ci ne?”
Rekel je: »Kdo ti je povedal, da si bil nag? Mar si jedel od drevesa, od katerega sem ti zapovedal, da ne bi smel jesti?«
12 Mutumin ya ce, “Macen da ka sa a nan tare da ni, ita ta ba ni waɗansu’ya’ya daga itacen, na kuwa ci.”
Mož je rekel: »Ženska, ki si mi jo dal, da je z menoj, ona mi je dala od drevesa in sem jedel.«
13 Sai Ubangiji Allah ya ce wa matar, “Me ke nan kika yi?” Matar ta ce, “Macijin ne ya ruɗe ni, na kuwa ci.”
Gospod Bog je rekel ženski: »Kaj je to, kar si storila?« Ženska je rekla: »Kača me je preslepila in sem jedla.«
14 Saboda haka Ubangiji Allah ya ce wa macijin, “Saboda ka yi haka, “Na la’anta ka cikin dukan dabbobi da kuma cikin dukan namun jeji! Daga yanzu rubda ciki za ka yi tafiya turɓaya kuma za ka ci dukan kwanakin rayuwarka.
Gospod Bog je rekel kači: »Ker si to storila, si prekleta nad vso živino in nad vsako poljsko živaljo. Po svojem trebuhu boš šla in prah boš jedla vse dni svojega življenja.
15 Zan kuma sa ƙiyayya tsakaninka da macen, tsakanin zuriyarka da zuriyarta. Zai ragargaje kanka, kai kuma za ka sari ɗiɗɗigensa.”
Postavil bom sovraštvo med teboj in žensko in med tvoje seme in njeno seme; to ti zdrobi glavo, ti pa boš ranila njegovo peto.«
16 Sa’an nan ya ce wa macen, “Zan tsananta naƙudarki ainun, da azaba kuma za ki haifi’ya’ya. Za ki riƙa yin marmarin mijinki zai kuwa yi mulki a kanki.”
Ženski je rekel: »Silno bom pomnožil tvojo bridkost in tvoje spočetje. V bridkosti boš rojevala otroke, in tvoje hrepenenje bo k tvojemu soprogu in on bo vladal nad teboj.«
17 Ga Adamu kuwa ya ce, “Saboda ka saurari matarka, ka kuma ci daga itacen da na ce, ‘Kada ka ci,’ “Za a la’anta ƙasa saboda kai. Da wahala za ka ci daga cikinta dukan kwanakin rayuwarka.
Adamu pa je rekel: »Ker si prisluhnil glasu svoje žene in si jedel od drevesa, o katerem sem ti zapovedal, rekoč: ›Ne boš jedel od njega; ‹ prekleta so tla zaradi tebe, v bridkosti boš jedel od le-teh vse dni svojega življenja.
18 Za tă ba ka ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya za ka kuwa ci ganyayen gona.
Tudi trnje in osat ti bodo obrodila; in poljsko zelišče boš jedel;
19 Da zuffan goshinka za ka ci abincinka har ka koma ga ƙasa, da yake daga cikinta aka yi ka. Gama kai turɓaya ne, kuma ga turɓaya za ka koma.”
v potu svojega obraza boš jedel kruh, dokler se ne vrneš v tla, kajti od tam si bil vzet, kajti prah si in v prah se boš vrnil.«
20 Mutumin ya sa wa matarsa suna, Hawwa’u, gama za tă zama mahaifiyar masu rai duka.
Adam je svojo ženo imenoval Eva; ker je bila mati vseh živih.
21 Ubangiji Allah ya yi tufafin fata domin Adamu da Hawwa’u, ya kuma yi musu sutura.
Adamu in njegovi ženi je Gospod Bog naredil plašča iz kož ter ju oblekel.
22 Ubangiji Allah ya kuma ce, “To, fa, mutum ya zama kamar ɗaya daga cikinmu, ya san abin da yake mai kyau da abin da yake mugu. Kada a yarda yă miƙa hannunsa yă ɗiba daga itacen rai yă ci, yă kuma rayu har abada.”
Gospod Bog je rekel: »Glej, človek je postal kakor eden izmed nas, da pozna dobro in zlo. In sedaj, da ne iztegne svoje roke in vzame tudi od drevesa življenja ter jé in živi na veke, «
23 Saboda haka Ubangiji Allah ya kore shi daga Lambun Eden domin yă nome ƙasa wadda aka yi shi.
ga je Gospod Bog zato odposlal iz edenskega vrta, da orje tla, iz katerih je bil vzet.
24 Bayan da ya kori mutumin, sai ya sa kerubobi da takobi mai harshen wuta yana jujjuyawa baya da gaba a gabashin Lambun Eden don yă tsare hanya zuwa itacen rai.
Tako je izgnal človeka in na vzhodu edenskega vrta namestil kerube in ognjen meč, ki obrača vsako pot, da varuje pot drevesa življenja.

< Farawa 3 >