< Farawa 25 >
1 Ibrahim ya auro wata mace, mai suna Ketura.
Abraham prit encore une autre femme du nom de Cettura.
2 Ta haifa masa Zimran, Yokshan, Medan, Midiyan, Ishbak da Shuwa.
Elle lui enfanta Zameran, Jezan, Madal, Madian, Jesboc et Sué.
3 Yokshan shi ne mahaifin Sheba da Dedan. Zuriyar Dedan su ne mutanen Ashur, da mutanen Letush, da kuma mutanen Lewummin.
Jezan engendra Saba et Dedan; fils de Dedan: Assurini, Latusim. et Laomim.
4 ’Ya’yan Midiyan maza su ne, Efa, Efer, Hanok, Abida, da kuma Elda’a. Dukan waɗannan zuriyar Ketura ce.
Fils de Madian: Gephar, Aphir, Énoch, Abida et Elduga. Tous ceux-ci étaient issus de Cettura.
5 Ibrahim ya bar wa Ishaku kome da ya mallaka.
Or, Abraham donna tout ce qu'il possédait à Isaac, son fils.
6 Amma yayinda Ibrahim yake da rai, ya ba wa’ya’yan ƙwarƙwaransa maza kyautai, ya kuma sallame su daga ɗansa Ishaku zuwa ƙasashen gabas.
Quant aux fils de ses concubines, Abraham leur fit des présents de son vivant, il les envoya loin de son fils Isaac, à l'orient, en la terre des Orientaux.
7 Duka-duka, Ibrahim ya yi shekara ɗari da saba’in da biyar.
Bientôt le nombre des jours que vécut Abraham forma cent soixante-cinq ans.
8 Sa’an nan Ibrahim ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu da kyakkyawar tsufa, tsoho da kuma shekaru masu yawa; aka kuma tara shi ga mutanensa.
Et Abraham mourut dans une belle vieillesse, âgé et plein de jours, et il fut réuni à son peuple.
9 ’Ya’yansa maza kuwa Ishaku da Ishmayel suka binne shi cikin kogon Makfela, kusa da Mamre, a cikin filin Efron ɗan Zohar mutumin Hitti,
Isaac et Ismaël, ses fils, l'ensevelirent en la double caverne dans le champ de l'Hettéen Éphron, fils de Saar, en face de Membré.
10 filin da Ibrahim ya saya daga Hittiyawa. A nan aka binne Ibrahim tare da matarsa Saratu.
C'était le champ et la caverne qu'Abraham avait achetés des fils de Het; ils y ensevelirent Abraham, auprès de sa femme Sarra.
11 Bayan rasuwar Ibrahim, Allah ya albarkaci ɗansa Ishaku wanda a lokacin yana zama kusa da Beyer-Lahai-Royi.
Or après la mort d'Abraham, Dieu bénit son fils Isaac, qui demeura vers le puits de la Vision.
12 Waɗannan su ne zuriyar Ishmayel ɗan Ibrahim, wanda Hagar mutuniyar Masar, baranyar Saratu, ta haifa wa Ibrahim.
Voici les générations d'Ismaël, fils d'Abraham, que lui enfanta l'Égyptienne Agar, servante de Sarra.
13 Ga jerin sunayen’ya’yan Ishmayel maza bisa ga haihuwarsu, Nebayiwot ɗan farin Ishmayel, Kedar, Adbeyel, Mibsam,
Voici les noms des fils d'Ismaël, conformes aux noms de leurs tribus: Nabaïoth, le premier-né d'Ismaël, puis Cédar, Abdéel, Massan,
15 Hadad, Tema, Yetur, Nafish da Kedema.
Puis Choddan, Théman, Jéthur, Naphis et Cedma.
16 Waɗannan su ne’ya’yan Ishmayel maza, waɗanda kuma suke sunayen kabilu goma sha biyu masu mulki bisa ga wuraren zamansu da sansaninsu.
Ceux-ci sont les fils d'Ismaël; ces noms sont ceux qu'ils portèrent sous leurs tentes, dans leurs camps; ils formèrent douze chefs d'autant de nations.
17 Duka-duka Ishmayel ya yi shekara ɗari da talatin da bakwai; sai ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu, aka kuma tara shi ga mutanensa.
Ismaël vécut cent trente-sept ans, et il mourut, et il fut réuni à sa race.
18 Zuriyarsa sun zauna tsakanin Hawila ne da Shur, wanda yake kusa da gabashin iyakar Masar wajen Asshur. Sun yi zaman rikici da dukan sauran’yan’uwansu.
Il avait demeuré entre Hévilat et Sur, qui est en face de l'Égypte, du côté des Assyriens, vis-à-vis de ses frères.
19 Waɗannan su ne zuriyar Ishaku ɗan Ibrahim. Ibrahim ya haifi Ishaku,
Voici les générations d'Isaac, fils d'Abraham. Abraham engendra Isaac.
20 Ishaku yana da shekara arba’in sa’ad da ya auri Rebeka’yar Betuwel, mutumin Aram, daga Faddan Aram,’yar’uwar Laban mutumin Aram.
Or, Isaac avait quarante ans lorsqu'il prit pour femme Rébécca, fille de Bathuel, le Syrien, de la Mésopotamie syrienne, sœur de Laban, le Syrien.
21 Ishaku ya yi addu’a ga Ubangiji a madadin matarsa, saboda ba ta haihuwa. Ubangiji ya amsa addu’arsa, matarsa Rebeka kuwa ta yi ciki.
Isaac pria au sujet de sa femme Rébécca, parce qu'elle était stérile; et le Seigneur l'exauça; Rébécca conçut.
22 Jariran suka kama kokawa da juna a cikinta, sai ta ce, “Me ya sa wannan yake faruwa da ni?” Saboda haka ta tafi don ta nemi nufin Ubangiji.
Comme deux enfants s'agitaient en ses entrailles, elle dit: Cela devait- il m'arriver? pourquoi cela m'arrive-t-il? Et elle s'en alla interroger le Seigneur.
23 Ubangiji ya ce mata, “Al’ummai biyu suna a cikin mahaifarki mutum biyu da za ki haifa, za su rabu da juna, ɗayan zai fi ɗayan ƙarfi, babban kuma zai bauta wa ƙaramin.”
Le Seigneur lui dit: Deux nations sont en ton sein; deux peuples en sortiront pour se séparer; l'un dominera l'autre, et le plus grand sera soumis au moindre.
24 Da lokaci ya yi da za tă haihu, sai ga’yan biyu maza a mahaifarta.
Et les jours de l'enfantement étant accomplis, elle se trouvait avoir deux jumeaux en ses entrailles.
25 Wanda ya fara fita ja ne, dukan jikinsa kuwa kamar riga mai gashi. Don haka aka sa masa suna Isuwa.
Le premier-né sortit roux, tout velu, semblable à une peau de bête fauve; et elle lui donna le nom d'Esaü.
26 Bayan wannan, ɗan’uwansa ya fito, da hannunsa yana riƙe da ɗiɗɗigen Isuwa; don haka aka sa masa suna Yaƙub. Ishaku yana da shekara sittin, lokacin da Rebeka ta haife su.
Après lui sortit son frère, sa main tenait le pied d'Esaü; aussi lui donna-t-elle le nom de Jacob. Isaac avait cinquante ans, lorsque Rébécca les enfanta.
27 Yaran suka yi girma, Isuwa kuwa ya zama riƙaƙƙen maharbi, mutumin jeji, yayinda Yaƙub, shiru-shiru ne mai son zama a tentuna.
Les jeunes gens grandirent. Esaü fut un homme rustique, habile chasseur; Jacob fut un homme paisible, se plaisant à la maison.
28 Ishaku, mai son ci naman jeji, ya ƙaunaci Isuwa, amma Rebeka ta ƙaunaci Yaƙub.
Isaac affectionnait Esaü, parce qu'il se nourrissait de son gibier; mais Rébécca chérissait Jacob.
29 Wata rana sa’ad da Yaƙub yana dafa fate. Isuwa ya shigo daga jeji, da yunwa sosai.
Or, Jacob avait fait cuire un mets, comme Esaü arriva de la plaine, défaillant.
30 Ya ce wa Yaƙub, “Ina roƙonka, ka ɗan ɗiba mini faten nan! Ina fama da yunwa!” (Shi ya sa aka kira shi Edom.)
Et Esaü dit à Jacob: Laisse-moi manger de cette bouillie rousse; car je suis défaillant.
31 Yaƙub ya amsa ya ce, “Ka fara sayar mini da matsayinka na ɗan fari tukuna.”
Jacob répondit à Esaü: Cède-moi aujourd'hui ton droit d'aînesse.
32 Isuwa ya ce, “Duba, ina gab da mutuwa, me matsayina na ɗan fari zai yi mini?”
Esaü reprit: Je vais mourir; à quoi me sert mon droit d'aînesse?
33 Amma Yaƙub ya ce, “Ka rantse mini tukuna.” Don haka ya rantse masa, ya sayar da matsayinsa na ɗan fari ga Yaƙub.
Jacob lui dit: Prête-moi serment aujourd'hui, et son frère jura; ainsi le droit d'aînesse d'Esaü fut transmis à Jacob.
34 Sa’an nan Yaƙub ya ba wa Isuwa burodi da ɗan miyan lansir. Ya ci, ya sha, sa’an nan ya tashi ya tafi. Ta haka Isuwa ya yi banza da matsayinsa na ɗan fari.
Jacob donna donc à son frère du pain et de la bouillie de lentilles; Esaü mangea et il but; puis, s'étant levé, il partit, sans se mettre davantage en peine de son droit d'aînesse.