< Farawa 21 >

1 Ana nan sai Ubangiji ya nuna wa Saratu alheri kamar yadda ya ce, Ubangiji kuma ya yi wa Saratu abin da ya yi alkawari.
The Lord came to help Sarah as he'd said he would. The Lord did for Sarah what he'd promised.
2 Saratu ta yi ciki, ta kuma haifa wa Ibrahim ɗa a tsufansa; a daidai lokacin da Allah ya yi masa alkawari.
She became pregnant and had a son for Abraham when he was old, at the exact time God said she would.
3 Ibrahim ya sa wa ɗan da Saratu ta haifa masa suna Ishaku.
Abraham named their son Isaac.
4 Sa’ad da ɗansa Ishaku ya kai kwana takwas da haihuwa, sai Ibrahim ya yi masa kaciya, kamar yadda Allah ya umarce shi.
Abraham circumcised him when Isaac was eight days old, following God's command.
5 Ibrahim yana da shekara ɗari, sa’ad da aka haifa masa ɗansa Ishaku.
Abraham was 100 when Isaac was born.
6 Saratu ta ce, “Allah ya sa na yi dariya, kuma duk wanda ya ji game da wannan, zai yi dariya tare da ni.”
Sarah declared, “God has made me laugh, and all those who hear about this will laugh with me.”
7 Ta kuma ƙara da cewa, “Dā, wa zai iya ce wa Ibrahim, Saratu za tă yi renon yara? Duk da haka na haifar masa ɗa cikin tsufansa.”
She also said, “Would anyone have announced to Abraham that Sarah was going to have children to nurse? But now I have had a son for Abraham even when he was old!”
8 Yaron ya yi girma, aka kuma yaye shi, a ranar da aka yaye shi kuwa, Ibrahim ya yi babban biki.
The baby grew up, and on the day Isaac was weaned Abraham held a large feast.
9 Amma Saratu ta ga cewa yaron da Hagar, mutuniyar Masar ta haifa wa Ibrahim yana wa ɗanta Ishaku gori,
But Sarah noticed that Ishmael, Hagar the Egyptian's son she'd had for Abraham, was making fun of Isaac.
10 sai ta ce wa Ibrahim, “Ka kori baiwan nan tare da ɗanta, saboda ɗan baiwan nan ba zai taɓa raba gādo da ɗana Ishaku ba.”
So she went to Abraham and told him, “You have to get rid of this slave woman and this son of hers! A slave woman's son is not going to be one of your heirs and inherit together with my son Isaac!”
11 Al’amarin ya ɓata wa Ibrahim rai sosai domin zancen ya shafi ɗansa.
Abraham felt very bad about it because Ishmael was his son.
12 Amma Allah ya ce wa Ibrahim, “Kada hankalinka yă tashi game da yaron nan da kuma baiwarka. Ka saurari duk abin da Saratu ta faɗa maka, saboda ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.
But God told Abraham, “Don't feel bad about the boy and the slave woman. Do whatever Sarah tells you, because it's through Isaac that your descendants will be counted.
13 Zan ba ɗan baiwan nan al’umma shi ma, domin shi zuriyarka ne.”
Don't worry—I will also make the son of the slave woman into a nation because he's your son.”
14 Kashegari da sassafe sai Ibrahim ya ɗauki abinci da salkar ruwa, ya ba wa Hagar. Ya ɗora su a kafaɗunta, sa’an nan ya sallame ta da yaron. Ta kama hanyarta ta kuma yi ta yawo a cikin jejin Beyersheba.
Abraham got up early the next morning. He packed up some food and a skin of water which he gave to Hagar, putting them on her shoulder. Then he sent her and the boy away. She left and wandered through the Desert of Beersheba.
15 Sa’ad da ruwan da yake cikin salkan ya ƙare, sai ta ajiye yaron a ƙarƙashin wani ƙaramin itace.
When the water ran out, she left the boy under one of the bushes.
16 Sai ta tafi, ta zauna ɗan nesa da yaron, misalin nisan harbin baka, gama ta yi tunani ta ce, “Ba zan iya kallon yaron yana mutuwa ba.” Da ta zauna nesa da yaron, sai ta fara kuka.
She went and sat down some way off, a few hundred yards away, saying, “I can't bear to watch my son die!” As she sat down she burst into tears.
17 Allah kuwa ya ji yaron yana kuka, sai mala’ikan Allah ya kira Hagar daga sama ya ce mata, “Mene ne damuwarki, Hagar? Kada ki ji tsoro, Allah ya ji yaron yana kuka yayinda yake kwance a can.
God heard the boy's cries, and the angel of God called to Hagar from heaven and asked her, “What's the matter, Hagar? Don't be afraid! God has heard the boy crying from where he is.
18 Ki ɗaga yaron ki riƙe shi a hannu, gama zan mai da shi al’umma mai girma.”
Get up, go over and help the boy up, and encourage him, for I will make him into a great nation.”
19 Sa’an nan Allah ya buɗe idanunta ta ga wata rijiyar ruwa. Don haka sai ta tafi ta cika salkan da ruwa, ta kuma ba wa yaron ruwa ya sha.
God opened her eyes and she saw a well nearby. She went and filled the skin with water and gave the boy a drink.
20 Allah ya kasance da yaron, yayinda yake girma. Ya yi zama a jeji, ya kuma zama maharbi.
God blessed Ishmael and he grew up, living in the desert. He became a skilled archer.
21 Yayinda yake zama a Jejin Faran, sai mahaifiyarsa ta samo masa mata daga Masar.
He lived in the Desert of Paran. His mother chose a wife for him from the land of Egypt.
22 A lokacin nan Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka zo suka ce wa Ibrahim, “Allah yana tare da kai a ko mene ne kake yi.
Around this time Abimelech came with Phicol, the commander of his army, to see Abraham. “God blesses you in everything you do,” Abimelech said.
23 Yanzu ka rantse mini a nan a gaban Allah cewa, ba za ka yaudare ni ko’ya’yana ko kuma zuriyata ba. Ka nuna mini alheri, kai da ƙasar da kake zama baƙunci kamar yadda na nuna maka.”
“So swear to me right here and now that you won't betray me, my children, or my descendants. In the same way I've proved I'm trustworthy to you, do the same to me and my country where you're currently living.”
24 Ibrahim ya ce, “Na rantse.”
“I so swear,” Abraham replied.
25 Sa’an nan Ibrahim ya kawo kuka ga Abimelek game da rijiyar ruwan da bayin Abimelek suka ƙwace.
Then Abraham raised an issue with Abimelech of a well that Abimelech's servants had taken by force.
26 Sai Abimelek ya ce, “Ban san wanda ya yi wannan ba. Ba ka faɗa mini ba, ban kuwa taɓa ji ba, sai yau.”
“I don't know who did this, and you didn't mention it before. I haven't heard anything about it until today,” Abimelech responded.
27 Sai Ibrahim ya kawo tumaki da shanu ya ba wa Abimelek, sai su biyun suka yi yarjejjeniya.
Then Abraham gave Abimelech some of his sheep and cattle, and the two of them made an agreement.
28 Ibrahim ya ware’yan raguna bakwai daga cikin garke,
Abraham also separated out seven female lambs from the flock.
29 sai Abimelek ya ce wa Ibrahim, “Mene ne ma’anar’yan raguna bakwai da ka keɓe?”
“What are these seven female lambs for that you've separated from the flock?” Abimelech asked.
30 Ibrahim ya amsa ya ce, “Ka karɓi waɗannan’yan tumaki bakwai daga hannuna a matsayin shaida cewa ni ne na haƙa wannan rijiya.”
“I'm giving you these seven female lambs in return for your admission that I dug this well,” Abraham replied.
31 Saboda haka aka kira wurin Beyersheba, domin a nan ne su biyun suka yi rantsuwa.
That's why he called the place Beersheba, because the two of them swore and oath to each other.
32 Bayan da aka yi yarjejjeniya a Beyersheba, sai Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka koma ƙasar Filistiyawa.
After making the agreement at Beersheba, Abimelech and Phicol the commander of his army left and went home to the country of the Philistines.
33 Sai Ibrahim ya shuka itacen tsamiya a Beyersheba, a can kuma ya kira bisa sunan Ubangiji, Allah Madawwami.
Abraham planted a tamarisk tree in Beersheba and there he worshiped the Lord, the Eternal God.
34 Ibrahim kuwa ya zauna a ƙasar Filistiyawa na dogon lokaci.
Abraham lived in the country of the Philistines for a long time.

< Farawa 21 >