< Farawa 2 >

1 Ta haka aka gama yin sammai da duniya da dukan abubuwan da suke cikinsu.
And the heavens and the earth are completed, and all their host;
2 Kafin kwana ta bakwai, Allah ya gama aikin da yake yi, saboda haka a kwana ta bakwai, ya huta daga dukan aikinsa.
and God completes by the seventh day His work which He has made, and ceases by the seventh day from all His work which He has made.
3 Allah kuwa ya albarkaci kwana ta bakwai, ya kuma mai da ita mai tsarki, saboda a kanta ne ya huta daga dukan aikin halittar da ya yi.
And God blesses the seventh day, and sanctifies it, for in it He has ceased from all His work which God had created for making.
4 Wannan shi ne asalin tarihin sammai da duniya sa’ad da aka halicce su. Sa’ad da Ubangiji Allah ya yi duniya da sammai,
These [are] the generations of the heavens and of the earth in their being created, in the day of YHWH God’s making the earth and the heavens;
5 babu tsiro a duniya kuma ganyaye ba su tsira a busasshiyar ƙasa ko ba, gama Ubangiji Allah bai aiko da ruwan sama a kan duniya ba tukuna, babu kuma wani mutumin da zai nome ƙasar,
and no shrub of the field is yet in the earth, and no herb of the field yet sprouts, for YHWH God has not rained on the earth, and there is not a man to serve the ground,
6 amma dai rafuffuka suna ɓullo da ruwa daga ƙasa suna jiƙe ko’ina a fāɗin ƙasa.
and a mist goes up from the earth, and has watered the whole face of the ground.
7 Sa’an nan Ubangiji Allah ya yi mutum daga turɓayar ƙasa, ya kuma hura numfashin rai cikin hancinsa, mutumin kuwa ya zama rayayyen taliki.
And YHWH God forms the man—dust from the ground, and breathes into his nostrils breath of life, and the man becomes a living creature.
8 To, fa, Ubangiji Allah ya yi lambu a gabas, a Eden, a can kuwa ya sa mutumin da ya yi.
And YHWH God plants a garden in Eden, at the east, and He sets there the man whom He has formed;
9 Ubangiji Allah ya kuma sa kowane irin itace ya tsira daga ƙasa, itace mai kyan gani, mai amfani kuma don abinci. A tsakiyar lambun kuwa akwai itacen rai da kuma itacen sanin abin da yake da kyau da abin da yake mugu.
and YHWH God causes to sprout from the ground every tree desirable for appearance, and good for food, and the Tree of Life in the midst of the garden, and the Tree of the Knowledge of Good and Evil.
10 Akwai wani kogi mai ba da ruwa ga lambun wanda ya gangaro daga Eden, daga nan ya rarrabu, ya zama koguna huɗu.
And a river is going out from Eden to water the garden, and from there it is parted, and has become four chief [rivers];
11 Sunan kogi na fari, Fishon. Shi ne yake malala kewaye da dukan ƙasar Hawila, inda akwai zinariya.
the name of the first [is] Pison, it [is] that which is surrounding the whole land of Havilah where the gold [is],
12 (Zinariyar wannan ƙasa kuwa tana da kyau, akwai kuma kayan ƙanshi da duwatsun da ake kira onis a can ma.)
and the gold of that land [is] good; the bdellium and the shoham stone [are] there;
13 Sunan kogi na biyu, Gihon. Shi ne ya malala kewaye da ƙasar Kush.
and the name of the second river [is] Gihon, it [is] that which is surrounding the whole land of Cush;
14 Sunan kogi na uku Tigris. Wannan ne ya malala ya bi ta gefen gabashin Asshur. Kogi na huɗu kuwa shi ne Yuferites.
and the name of the third river [is] Hiddekel, it [is] that which is going east of Asshur; and the fourth river is the Euphrates.
15 Ubangiji Allah ya ɗauko mutumin ya sa shi cikin Lambun Eden domin yă nome shi, yă kuma lura da shi.
And YHWH God takes the man, and causes him to rest in the Garden of Eden, to serve it and to keep it.
16 Ubangiji Allah ya umarci mutumin ya ce, “Kana da’yanci ka ci daga kowane itace a cikin lambun,
And YHWH God lays a charge on the man, saying, “From every tree of the garden eating you eat;
17 amma kada ka ci daga itacen sanin abin da yake mai kyau da abin da yake mugu, gama a ranar da ka ci shi, lalle za ka mutu.”
but from the Tree of the Knowledge of Good and Evil, you do not eat from it, for in the day of your eating from it—dying you die.”
18 Ubangiji Allah ya ce, “Bai yi kyau mutumin yă kasance shi kaɗai ba. Zan yi masa mataimakin da ya dace da shi.”
And YHWH God says, “[It is] not good for the man to be alone; I make him a helper as his counterpart.”
19 To, Ubangiji Allah ya yi dukan namun jeji da dukan tsuntsayen sama daga ƙasa. Ya kawo su wurin mutumin don yă ga wanda suna zai kira su; kuma duk sunan da mutumin ya kira kowane mai rai, sunansa ke nan.
And YHWH God forms from the ground every beast of the field, and every bird of the heavens, and brings [them] to the man, to see what he calls it; and whatever the man calls a living creature, that [is] its name.
20 Saboda haka mutumin ya sa wa dukan dabbobi, da tsuntsayen sama da dukan namun jeji sunaye. Amma ba a sami mataimakin da ya dace da Adamu ba.
And the man calls names to all the livestock, and to bird of the heavens, and to every beast of the field; but for man a helper has not been found as his counterpart.
21 Saboda haka Ubangiji Allah ya sa mutumin ya yi barci mai nauyi; yayinda yake barci sai ya ɗauko ɗaya daga cikin haƙarƙarin mutumin, ya kuma rufe wurin da nama.
And YHWH God causes a deep sleep to fall on the man, and he sleeps, and He takes one of his ribs, and closes up flesh in its stead.
22 Sa’an nan Ubangiji Allah ya yi mace daga haƙarƙarin da ya ɗauko daga mutumin, ya kuwa kawo ta wurin mutumin.
And YHWH God builds up the rib which He has taken out of the man into a woman, and brings her to the man;
23 Sai mutumin ya ce, “Yanzu kam wannan ƙashi ne na ƙasusuwana nama kuma na namana. Za a ce da ita ‘mace,’ gama an ciro ta daga namiji.”
and the man says, “This at last! Bone of my bone, and flesh of my flesh!” For this is called Woman, for this has been taken from Man;
24 Wannan ne ya sa mutum yakan bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa, su kuma zama jiki ɗaya.
therefore a man leaves his father and his mother, and has cleaved to his wife, and they have become one flesh.
25 Mutumin da matarsa, dukansu biyu tsirara suke, ba su kuwa ji kunya ba.
And both of them are naked, the man and his wife, and they are not ashamed of themselves.

< Farawa 2 >